• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Ta Kori Ma’aikata 2 Kan Amfani Da Takardun Bogi Don Cinye Kudin Mamaci

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Bauchi Ta Kori Ma’aikata 2 Kan Amfani Da Takardun Bogi Don Cinye Kudin Mamaci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula Da Ma’aikata ta jihar Bauchi ta sake korar wasu ma’aikatan gwamnati biyu masu suna Nasiru Samaila da Anas Jibrin bisa samunsu da laifin amfani da takardun bogi domin cinye ma wani mamacin kudadensa. 

Ma’aikatan biyu, su na aiki ne a karkashin ma’aikatar kudi ta jihar an zargesu da karkatarwa da sama da fadi da naira N332, 000 mallakin wani tsohon ma’aikatacin ma’aikatar Jibrin Adamu Zalanga (wanda ya rasu ma a halin yanzu) wanda a cewar hukumar, wannan dabi’ar ta saba wa sashin dokokin aikin gwamnati sashi na 327.

  • Wakilin Jaridar Leadership Na Kano Ya Rasu
  • Kalubalen Hada Kan ‘Ya’yan Jam’iyyar APC Da Ke Gaban Ganduje 

Hukumar ta cimma wannan matsalar korar nasu ne a yayin zamanta karo na 18 da ya gudana a ranar 15 ga watan Agustan 2023.

A sanarwar manema labarai da jami’in yada labarai na hukumar Saleh Umar ya fitar a ranar Juma’a ya ce, “A yayin zaman da hukumar ta yi kan kes din kwamitin kula da ladabtarwa, ma’aikata guda biyu wanda aka samu da laifin amfani da takardun jabu domin samun damar karkatar da kudi da yawansu ya kai N332,000 mallakin wani tsoho kuma marigayin ma’aikacin ma’aikatar kudi na jihar Bauchi (Jibrin Adamu Zalanga)”.

“Wannan matakin nasu ya saba wa sashi 327 na dokokin tsarin aikin gwamnati kuma jami’an biyu sun amsa laifukansu a yayin amsa tambayoyin da ma’aikatar ta musu,” Umar ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Malam Saleh Umar ya yi kuma yi bayanin cewa tun da farko ‘yansanda sun kama ma’aikatan biyu tare da gurfanar da su a gaban babban kotun majistire domin samun hukunci daidai da laifukansu.

A cewarsa a yayin zaman hukumar ta kuma amince da karin girma ga wasu jami’ai 73 bisa kwazonsu da cancantarsu, kana an yi sauyi ga wasu mutum 11.

Shugaban hukumar, Alhaji Abubakar Usman Madakin Bunun Bauchi wanda ya jagoranci zaman, ya ce, kesa-kesan badakar kudade da suke samu na matukar damunsu.

Ya gargadi ma’aikata da suke jin tsoron Allah a dukkanin ayyukansu inda ya ce duk wanda ya kuma ki ji to ba zai ki gani ba.

A fadinsa za su kara sanya ido wajen dakile irin wannan mummunar dabi’ar.

Idan za ku tuna dai a kwanakin baya hukumar ta dakatar da izinin daukan aikin Ibrahim Garba wanda ma’aikaci ne a hukumar kula da fansho ta jihar bisa kamasa da laifin cinye kudin wani mamacin dan fansho.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Tallafawa Ci Gaban Afirka Nauyi Ne Na Bai Daya Da Ya Rataya A Wuyan Kasashen Duniya

Next Post

Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

28 minutes ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

5 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

6 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

7 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

9 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

12 hours ago
Next Post
Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al'umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

LABARAI MASU NASABA

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.