• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Zamfara

A ƙalla ƴan bindiga 37 ne aka kashe a ƙauyen Matusgi dake ƙaramar hukumar Talata Mafara a jihar Zamfara, bayan mazauna yankin sun kai farmaki kan wata tawagar ƴan bindiga da suka mamaye ƙauyen da nufin sace mazauna yankin.

Wani mazaunin yankin ya ce ƴan bindigar, waɗanda suka iso ƙauyen a kan babura da misalin ƙarfe 2 na rana a ranar Laraba, sun fara harbe-harbe don tsoratar da mutanen ƙauyen. Sai dai, mutanen yankin da suka yi shiri da bindigogin gargajiya da makamai na al’ada sun fuskanci maharan kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

  • An Kammala Gasar Tseren Dawakai Ta Ƙasa-da-ƙasa A Jihar Kano
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

Fafatawar ta ɗauki tsawon sa’a guda, inda mutanen ƙauyen suka samu nasarar kashe ƴan bindiga 10, hakan ya tilasta suka janye. Daga nan ne mutanen yankin suka sake haɗuwa suka yi kwanton ɓauna, wanda ya haifar da sake kashe ƙarin ƴan bindiga 27 yayin da suka dawo.

Zamfara

Hakimin Matusgi, Alhaji Ciroma Muhammad, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya kuma bayyana cewa mutane uku daga cikin mazauna yankin sun rasa rayukansu yayin artabun.

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

Alhaji Muhammad ya kuma nuna damuwa cewa wannan hari shi ne karo na 13 da ƴan bindiga suka kai wa ƙauyen. Ya yi karin bayani kan wani harin da ya faru makonni uku da suka gabata, inda aka yi garkuwa da mutane 23, galibinsu mata, kuma aka buƙaci fansar Naira 150,000 a kan kowane mutum.

Duk da biyan kuɗin, an sako mata bakwai kaɗai, yayin da ragowar ke ci gaba da zama a hannun masu garkuwa da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Zamfara
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Next Post
Sai Yaushe Matatar Man Fetur Ta Fatakwal Za Ta Fara Aiki?

Sai Yaushe Matatar Man Fetur Ta Fatakwal Za Ta Fara Aiki?

LABARAI MASU NASABA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Zamfara

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.