ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sai Yaushe Matatar Man Fetur Ta Fatakwal Za Ta Fara Aiki?

by Ra'ayinmu
2 years ago
Fetur

Gazawar kamfanin NNPCL na cika alkawarin da yayi na fara aikin daya daga cikin matatu hudu na man fetur na kasa da suka zama tamkar yanzu mutum yanzu ba mutum ba, (Matatar Mai ta Fatakwal an ce zata fara aiki bada dadewa ba).Wani abu ne da yake tayar da hankalin al’ummar Nijeriya, musamman ma masu yi wa kasa fatan alhairi.

Idan za a iya tunawa kamfanin NNPCL ya yi ta sa ranar da cewa matatar man za ta fara aiki lokuttan baya amma sai aka kasa cika alkawarin ba kuma tare da wani kwakkwaran dalili ba.Daga watan Disamba na shekarar 2023 zuwa yanzu NNPCL ya bayar da ranaku da dama na fara aikin matatar man da ake sa ran za ta rika tace danyan mai fiye da ganga 210,000 a kullum amma har yanzu babu wata alamar fara yin aikin matatar man.

  • Ma’aikatan NNPC Ba Barayi Ba Ne – Mele Kyari
  • Mun Gano Hanyoyin Da Ake Satar Man Fetur A Nijeriya – NNPC

A watan jiya ne, shugaban kamfanin NNPCL, Mele Kyari ya sanar da cewa, matatar man za ta fara aiki a farkon watan Agusta. Ga mu muna gab da fita watan Agustan amma har yanzu farkon watan Agustan Kyari bai yi ba kuma har yanzu matatar man na nan bata fara aiki ba.

ADVERTISEMENT

A watan Maris na shekarar 2021, gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ta bayar da kwangilar Dala Biliyan 1.5 ga wani kamfanin kasar Italiya mai suna Tecnimont SPA, domin yi wa matatar man kwaskwarima,an kasa aikin kashi uku da alkawarin kammala shi a cikin wata 18, 24,da kuma 44.An samar da wasu kamfanonin kasar Italiya; Maire Tecnimont da Oil Major Eni a matsayin wadanda za su tallafa wajen gudanar da aikin gaba daya.

Bayan tabbaci a lokutta da dama na fara aikin matatar man, a halin yanzu dole ‘yan Nijeriya za su kara jira na wani lokaci mai tsawo kafiin hakan ta faru. Amma kuma menene dalilin na gazawar NNPCL na bayar da cikakken dalili ga al’ummar Nijeriya a kan ita gazawar cika wancan alkawarin da ta dade tana yi wa al’ummar kasa a kan fara aikin matatar mai ta Fatakwal?

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Tabbas, rashin cika alkawarin da aka yi na fara aikin matatar man Fatakwal wani abu ne da ke da alaka da halayyar shugabannin kasar nan, inda shugabanin ke yin alkawari amma sai su ki cikawa, kuma babu wanda zai kama su da wani laifi.A gare su babu wanda ya isa ya kama su da wani laifi, in ba haka ba ai da an kama wani da laifin rashin cika alkawarin tare da hukunta ko wanene shi ko kuma a bayar da kwakkwaran dalilin da ya hana cika alkawarin, musamman ganin alkawurran sun yi yawa.

Amma me zai sa Nijeriya ta damu da rashin aikin matatar man ta Fatakwal da sauran matatun mai na sassan kasar? Wannan na da muhimmanci musamman ma ganin irin makudan kudaden da ake kashewa wajen sayo tataccen man fetur daga kasashen waje.Bayan madudan kudaden da ake tarawa na haraji hakan kuma na dora nauyi a kan naira saboda da kudaden kasashen waje (Dala) ake harkar sayen man fetur daga kasashen waje.

Ministan kudi da tattalin arzikin Nijeriya, Mister Wale Edun, ya bayyana cewa, Nijeriya na kashe fiye da dala miliyan 600 wajen shigo da man fetur a kowane wata.

In har Nijeriya na kashe wadannan kudaden wajen shigo da man fetur to lalle babu dalilin da zai sa NNPCL ta yi wasa wajen tabbatar da matatar man Fatakwal ta fara yin aiki, da sauran matatun man da ake su a sassan kasar Nijeriya.

Akwai tashin hankali matuka duk da dimbin man fetur da kasar nan take da shi amma har yanzu kasar nan ta dogara ne da shigo da man fetur,(ana shigo fiye da kashi 80 na albarkatun man fetur da kasa ke bukata daga kasashen waje).

Gyara tare da yi wa matatar mai ta Fatakwal kwaskwarima wata dama ce da kasar nan za ta rage kudaden da take kashewa wajen shigo da tacaccen man fetur a kan haka dole a hada tare yin duk kokarin da ya kamata na ganin matatar man Fatakwal ta fara aiki ba tare da bata lokaci ba.

Ya kamata mu yi koyi da kasa ta biyu a yawan man fetur a Afirka wato Angola, wadda a halin yanzu ta yi nisa wajen gina karin matatun mai a fadin kasar duk kuwa da tana da matatar mai tace fiye da 65,000 a kullum a garin Luanda.

A halin yanzu Angola na gina sabbin matatun mai guda uku a garuruwan Cabinda, Lobito, da Soyo. Yayin da ake sa ran kaddamar da matatar mai ta Cabinda zuwa karshen wannan shekarar, za a kaddamar da matatun mai na Lobito da Soyo a cikin shekara 2025. Shirin su shi ne kara man da suke tacewa a cikin gida zuwa ganga 400,000 a kowace rana.

Duk da cewa, dokokin kasa sun amincewa samar da matatun mai masu zaman kansu, a halin yanzu matatun masu zaman kansu irin su na Dangote sun fara aiki, bukatar ganin matatun mai na gwamnati sun fara aiki na da muhimmancin gaske. Tabbatar da wadatuwar man fetur a kasa na bukatar sa hannun gwamnati musamman tabbatar da ganin matatun man fetur na kasar mu suna aiki yadda ya kamata.

A kwanan nan ne aka zargi NNPC Limited da bangaren samar da mai da iskar gas na kasa kan yadda ake samun tsadar man fetur da kuma dambarwar da aka yi a kan shirin sayarwa matatar mai ta Dangote danyen mai.

‘Yan Nijeriya na da gaskiya in suka yi tsaye suka nemi da a tabbatar da matatar mai ta Fatakwal ta fara aiki nan take musamman ma ganin ta lamushe fiye da dala biliyan 1.5 tun da aka fara maganar gyara da yi mata kwaskwarima.Ba zai yiwu a ce Nijeriya na kashe dimbin kudade wajen shigo da man fetur amma kuma ana sayar da litar man a kan Naira 1,000, bayan wasu matatun na cikin gida sun yi alkawarin samar da sauki a farashin man ba.

Muna kira ga NNPCL da ta bayyana cikakken halin da matatar man Fatakwal take ciki, domin zuwa yanzu alkawurran da aka dauka na kammala gyaran ana karyawa ya yi yawa, mun kuma gaji haka.

Fetur
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Next Post
Kazancewar Matsalar Tsaro A Kwanan Nan…

Kazancewar Matsalar Tsaro A Kwanan Nan…

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.