Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Bayan Janye Yajin Malaman Jami’o’i: Babu Dalibai A Jami’ar Ahmadu Bello

by Tayo Adelaja
September 25, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Balarabe Abdullahi, Zariya

Kimanin kwanaki kenan da janye yajin aiki da Malaman jami’o’in Nijeriya suka yi. Wakilinmu ya sami damar zagaya sassan cibiyar jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya da kuma sashin Jami’ar da ke Kongo, inda ya tarar da babu dalibai a harabobin Jami’ar.

samndaads

Lokacin da wakilinmu ya nemi jin ta bakin masu wukar yankar magana na Jami’ar, hakarsa ba ta kai ga cimma ruwa ba, domin bai sami nasarar yin hakan ba, saboda wasu dalilai da suka hada da matakan ganin wadanda ya dace su ce wani abu kan yajin aikin ya yi tsauri ga wakilin namu.

Wani babban Malami da ke koyarwa a cibiyar Jami’ar ta Ahmadu Bello, wanda kuma ya nemi da wakilinmu ya sakaya sunansa ya ce, ba hakkin kungiyar Malamai ba ne su umurci dalibai su dawo harabar Jami’ar domin ci gaba daukar darussa, wannan hakkin mahukuntan Jami’ar ne.

Wakilinmu ya gano cewar, wasu kungiyoyin da suke Jami’ar, da suka hada da na manyan ma’aikata da kungiyar masu gudanar wasu ayyuka na musamman da dai wasu kungiyoyi na ci gaba da yajin aiki, a bisa wasu bukatu da suke neman gwamnatin tarayya ta biya masu shekaru da dama da suka gabata.

Wakilinmu ya gano cewar, ko da Malaman sun janye yajin aiki, mahukuntan Jami’ar babu yadda za a yi su kira dalibai daga gidajen iyayensu, domin kungiyoyin da aka ambata suna da matukar muhimmanci, domina babu yadda za a yi Malaman su gabatar da ayyukansu, ba tare da su ba.

Ammawasu labarai masu tushe sun ce wadannan kungiyoyi, sun sami matsaya a tsakaninsu da gwamnatin tarayya, wanda in sun amince da matsayar, akwai yiwuwar nan ba da jimawa ba mahukuntan Jami’ar za su kada gugen dawowar daliban domin su ci gaba daukar darussasu.

Har ila yau wakilinmu ya gano cewar a duk lokacin da daliban suka koma harabar Jami’ar, ba za a dauki lokaci mai tsawo ba za su fara jarabawa a daukacin cibiyoyi da kuma tsangayoyin da suke Jamai’ar a Samaru da kuma Kongo.

Wani dalibi da ke nazarin aikin jarida ya shaida wa wakilinmu cewar, wannan yajin aiki da Malaman da kuma sauran kungiyoyin ma’aikatan Jami’ar ke yi ya kawo masu babbar cikas ga karatun da suke yi, musamman da zarar sun dawo, ba za su dauki dogon lokaci ba za su fara jarabawa.

SendShareTweetShare
Previous Post

LEADERSHIP A Yau Za Ta Taimaka Wa Daliban Kwalejin Horas Da Malamai —Dakta Baraka Abubakar

Next Post

Zaben 2019: Ba Mu Da ‘Yan Takara Sai Buhari Da Masari — Jam’iyyar APC

RelatedPosts

Allurar Rigakafin Kurona

An Yi Kira Ga ‘Yan Nijeriya Da Su Rungumi Allurar Rigakafin Kurona Da Zarar An Fara

by Sulaiman Ibrahim
5 mins ago
0

An yi kira ga al"umar kasar nan su yi amfani...

Buhari

Buhari Ya Yi Wa Sultan Ta’aziyyyar Rasuwar Dan Uwansa

by Sulaiman Ibrahim
10 mins ago
0

Shugaba Muhammadu Buhari ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Abdulkadir Jeli...

Ambaliyar Ruwa

Manoma 35,000 Suka Amfana Da Tallafin Kayan Aikin Gona A Jihar Jigawa

by Sulaiman Ibrahim
13 mins ago
0

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Jigawa ta bayyana...

Next Post

Zaben 2019: Ba Mu Da ‘Yan Takara Sai Buhari Da Masari — Jam’iyyar APC

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version