• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bin Diddigi: Da Gaske Gwamnati Ta Kashe Naira Biliyan 5.9 A Horas Da Matasa 177 Gyaran Wayar Hannu?

by Musa Muhammad
3 years ago
gwamnati

Ikirari: Kwanan nan aka yada wani hoto da aka nuna “shafin farko” ne na jaridar PUNCH a soshiyal midiya inda aka nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta kashe zunzurutun kudi har naira biliyan 5 da miliyan dari tara (N5.9bn) wajen horas da matasa guda 177 kan yadda ake gyaran wayar hannu.

Cikakken Labarin: A wannan “shafin farkon” da aka yada, an rubuta baro-baro cewa, “Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta kashe naira biliyan 5.9 wajen horas da matasa 177 kan gyaran wayar hannu,” labarin da ya jawo maganganu da suka mai yawan gaske daga ‘yan Nijeriya.

  • Da Dumi-dumi: Atiku Ya Gana Da Wike A Landan

Wani mai amfani da Instagram ya yi tsokaci a kan zancen inda ya ce, “Don Allah ko akwai wanda zai ba ni ruwan sha kofi daya, Nijeriya ta kusa sanya ni in suma! Ban da dukkan rancen kudin da ake karbowa, in ba a ce dabbobi ba, beraye da kwari sai kuma a ce … wai har yanzu biliyan na da ziro guda tara ne? Akwai bukatar mu #sakekarbarnaija #tsaftacenaija #sakeginanaija.”

Wani kuma ya hau Tuwita ya yi tsokaci kamar haka: “Do Allah, ko akwai gwanayen lissafi a nan? Don Allah ku lissafa, ina so in ga nawa ne ake nufin APC ta kashe a kan wadannan matasan bogin su 177?
“Ya ku Matasa, kafin ku goyi bayan haukan nan da ake kira APC, ku tuna da wannan kanun labarin. In da an yi amfani da wannan kudin ta hanyar da ta dace, ai da mun samu matasa masu amfanarwa.”

Tabbaci: Jaridar PRNigeria ta lura da cewa wannan hoton ya na da tambarin ‘watermark’ “- 6mdh – photogrid” wanda ya sa ake ganin sa kamar tambarin jaridar PUNCH na gaske ne aka dauko daga masu amfani da soshiyal midiya daban-daban, saboda haka sai mu ka yi amfani da hikimar bincike ta ‘reberse image search’ a manhajar Google, a karshe sai sakamakon ya nuna mana cewa hoton wanda ya yi kama da na bangon gaba na mujalla babu inda ya fito a cikin shafukan zahiri na jaridar PUNCH da ke soshiyal midiya, kawai wasu masu amfani da shafukan zumunta ne su ka rika tura shi nan da can a Tuwita da Instagram.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Daga nan jaridar PRNigeria ta tuntubi sashen yada labarai na Ma’aikatar Harkokin Jinkai domin tabbatar da gaskiyar wannan magana, to amma sai wani jami’i da ya roki mu sakaya sunan sa ya bayyana lamarin da “Labarin bogi.”

Sai dai da PRNigeria ta gudanar da bincike kan wasu muhimman kalmomi a wurare daban-daban, ta gano cewa duk da yake hoton da aka yada karya ne, shi labarin ba karya ba ne amma kuma rahoto ne da ya fito watanni hudu da su ka gabata.
Gaskiya ne cewa Gwamnatin Tarayya ta bayyana a cikin Afrilu 2022 cewa ta ware kudi naira biliyan N5.9 domin horaswa da samar da kayan aiki da biyan alawus-alawus a kowane wata kan Rukunin C na shirin ‘N-Power’ a Jihar Kano, ba wai a kan matasa 177 kacal ba. Gwamnatin ta nanata cewa kimanin matasa 16,629 ne su ke amfana da shirin (karkashin Rukunin C) a jihar, ta kara da cewa a kiyasi har mutum 18,042 sun ci moriyar shirin a Rukunin A da na B na shirin.

Ministar Harkokin Jinkai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouk, ita ce ta ba da wannan bayanin ta hannun Mai Taimaka wa Shugaban Kasa na Musamman a Koyar da Sana’o’i, Dakta Nasir Mahmoud, lokacin da ya wakilce ta a wajen bikin yaye daliban shirin ‘N-Skills’, wanda wani sashe ne na ‘N-Power’, wanda aka yi a Kano, inda aka horas da matasa 177 kan gyaran waya.

Wannan bayanin ne jaridar PUNCH ta dauka ta lauya shi ta buga labarin da ya yaudari masu karatu, wanda tuni ta gyara labarin.

Kammalawa: Bisa ga shaidar da jaridar PRNigeria ta harhada, mun gano cewa ikirarin wai Gwamnatin Tarayya ta kashe naira biliyan 5.9 kan horas da matasa guda 177 su iya gyaran waya ba gaskiya ba ne. An fara buga rahoton a cikin jaridar PUNCH (shi ma ba a shafin farko ba) wanda tuni sun gyara shi tunda matasa 177 din da ake magana wani sashe ne kadai daga cikin jimillar matasa 16,629 da za a horas a Rukunin C na shirin ‘N-Power’ a Jihar Kano wadanda za su amfana da naira biliyan 5.9 da Gwamnatin Tarayya ta kasafta. Haka kuma, hoton da ake yadawa ba daga ita kan ta jaridar PUNCH ya fito ba, kawai wasu ne su ka kirkire shi domin su yaudari jama’a.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Dinkewar Kasar Sin Babbar Nasara Ce Ga Daukacin Duniya

Dinkewar Kasar Sin Babbar Nasara Ce Ga Daukacin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 17, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025
Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
peter

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.