• English
  • Business News
Thursday, June 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bin Diddigi: Da Gaske Gwamnati Ta Kashe Naira Biliyan 5.9 A Horas Da Matasa 177 Gyaran Wayar Hannu?

by Musa Muhammad
3 years ago
in Rahotonni
0
gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ikirari: Kwanan nan aka yada wani hoto da aka nuna “shafin farko” ne na jaridar PUNCH a soshiyal midiya inda aka nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta kashe zunzurutun kudi har naira biliyan 5 da miliyan dari tara (N5.9bn) wajen horas da matasa guda 177 kan yadda ake gyaran wayar hannu.

Cikakken Labarin: A wannan “shafin farkon” da aka yada, an rubuta baro-baro cewa, “Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta kashe naira biliyan 5.9 wajen horas da matasa 177 kan gyaran wayar hannu,” labarin da ya jawo maganganu da suka mai yawan gaske daga ‘yan Nijeriya.

  • Da Dumi-dumi: Atiku Ya Gana Da Wike A Landan

Wani mai amfani da Instagram ya yi tsokaci a kan zancen inda ya ce, “Don Allah ko akwai wanda zai ba ni ruwan sha kofi daya, Nijeriya ta kusa sanya ni in suma! Ban da dukkan rancen kudin da ake karbowa, in ba a ce dabbobi ba, beraye da kwari sai kuma a ce … wai har yanzu biliyan na da ziro guda tara ne? Akwai bukatar mu #sakekarbarnaija #tsaftacenaija #sakeginanaija.”

Wani kuma ya hau Tuwita ya yi tsokaci kamar haka: “Do Allah, ko akwai gwanayen lissafi a nan? Don Allah ku lissafa, ina so in ga nawa ne ake nufin APC ta kashe a kan wadannan matasan bogin su 177?
“Ya ku Matasa, kafin ku goyi bayan haukan nan da ake kira APC, ku tuna da wannan kanun labarin. In da an yi amfani da wannan kudin ta hanyar da ta dace, ai da mun samu matasa masu amfanarwa.”

Tabbaci: Jaridar PRNigeria ta lura da cewa wannan hoton ya na da tambarin ‘watermark’ “- 6mdh – photogrid” wanda ya sa ake ganin sa kamar tambarin jaridar PUNCH na gaske ne aka dauko daga masu amfani da soshiyal midiya daban-daban, saboda haka sai mu ka yi amfani da hikimar bincike ta ‘reberse image search’ a manhajar Google, a karshe sai sakamakon ya nuna mana cewa hoton wanda ya yi kama da na bangon gaba na mujalla babu inda ya fito a cikin shafukan zahiri na jaridar PUNCH da ke soshiyal midiya, kawai wasu masu amfani da shafukan zumunta ne su ka rika tura shi nan da can a Tuwita da Instagram.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Daga nan jaridar PRNigeria ta tuntubi sashen yada labarai na Ma’aikatar Harkokin Jinkai domin tabbatar da gaskiyar wannan magana, to amma sai wani jami’i da ya roki mu sakaya sunan sa ya bayyana lamarin da “Labarin bogi.”

Sai dai da PRNigeria ta gudanar da bincike kan wasu muhimman kalmomi a wurare daban-daban, ta gano cewa duk da yake hoton da aka yada karya ne, shi labarin ba karya ba ne amma kuma rahoto ne da ya fito watanni hudu da su ka gabata.
Gaskiya ne cewa Gwamnatin Tarayya ta bayyana a cikin Afrilu 2022 cewa ta ware kudi naira biliyan N5.9 domin horaswa da samar da kayan aiki da biyan alawus-alawus a kowane wata kan Rukunin C na shirin ‘N-Power’ a Jihar Kano, ba wai a kan matasa 177 kacal ba. Gwamnatin ta nanata cewa kimanin matasa 16,629 ne su ke amfana da shirin (karkashin Rukunin C) a jihar, ta kara da cewa a kiyasi har mutum 18,042 sun ci moriyar shirin a Rukunin A da na B na shirin.

Ministar Harkokin Jinkai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouk, ita ce ta ba da wannan bayanin ta hannun Mai Taimaka wa Shugaban Kasa na Musamman a Koyar da Sana’o’i, Dakta Nasir Mahmoud, lokacin da ya wakilce ta a wajen bikin yaye daliban shirin ‘N-Skills’, wanda wani sashe ne na ‘N-Power’, wanda aka yi a Kano, inda aka horas da matasa 177 kan gyaran waya.

Wannan bayanin ne jaridar PUNCH ta dauka ta lauya shi ta buga labarin da ya yaudari masu karatu, wanda tuni ta gyara labarin.

Kammalawa: Bisa ga shaidar da jaridar PRNigeria ta harhada, mun gano cewa ikirarin wai Gwamnatin Tarayya ta kashe naira biliyan 5.9 kan horas da matasa guda 177 su iya gyaran waya ba gaskiya ba ne. An fara buga rahoton a cikin jaridar PUNCH (shi ma ba a shafin farko ba) wanda tuni sun gyara shi tunda matasa 177 din da ake magana wani sashe ne kadai daga cikin jimillar matasa 16,629 da za a horas a Rukunin C na shirin ‘N-Power’ a Jihar Kano wadanda za su amfana da naira biliyan 5.9 da Gwamnatin Tarayya ta kasafta. Haka kuma, hoton da ake yadawa ba daga ita kan ta jaridar PUNCH ya fito ba, kawai wasu ne su ka kirkire shi domin su yaudari jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kudaden Paris Club: Ana Ce-ce-ku-ce Tsakanin Gwamnoni Da Ministan Shari’a

Next Post

Dinkewar Kasar Sin Babbar Nasara Ce Ga Daukacin Duniya

Related

gwamnati
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

5 days ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

6 days ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

2 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

2 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

3 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Dinkewar Kasar Sin Babbar Nasara Ce Ga Daukacin Duniya

Dinkewar Kasar Sin Babbar Nasara Ce Ga Daukacin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025

June 12, 2025
Sin Na Fatan Amurka Ta Yi Hadin Gwiwa Da Ita Don Tabbatar Da Matsayar Da Shugabannin Kasashen Biyu Suka Cimma

Sin Na Fatan Amurka Ta Yi Hadin Gwiwa Da Ita Don Tabbatar Da Matsayar Da Shugabannin Kasashen Biyu Suka Cimma

June 12, 2025
Sin Ta sanya Indonesiya Cikin Tsarin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Na Sa’o’i 240 Da Kara Yawan Kasashen Tsarin Zuwa 55

Sin Ta sanya Indonesiya Cikin Tsarin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Na Sa’o’i 240 Da Kara Yawan Kasashen Tsarin Zuwa 55

June 12, 2025
Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka

June 12, 2025
Zambar Naira Miliyan 55: ICPC Ta Fara Bin Diddigin Dan Kwangilar Dam Din Jihar Filato

ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2

June 12, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 

Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 

June 12, 2025
De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

June 12, 2025
Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

June 12, 2025
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

June 12, 2025
An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha

An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha

June 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.