ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bin Diddigi: Da Gaske Gwamnati Ta Kashe Naira Biliyan 5.9 A Horas Da Matasa 177 Gyaran Wayar Hannu?

by Musa Muhammad
4 years ago
gwamnati

Ikirari: Kwanan nan aka yada wani hoto da aka nuna “shafin farko” ne na jaridar PUNCH a soshiyal midiya inda aka nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta kashe zunzurutun kudi har naira biliyan 5 da miliyan dari tara (N5.9bn) wajen horas da matasa guda 177 kan yadda ake gyaran wayar hannu.

Cikakken Labarin: A wannan “shafin farkon” da aka yada, an rubuta baro-baro cewa, “Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta kashe naira biliyan 5.9 wajen horas da matasa 177 kan gyaran wayar hannu,” labarin da ya jawo maganganu da suka mai yawan gaske daga ‘yan Nijeriya.

  • Da Dumi-dumi: Atiku Ya Gana Da Wike A Landan

Wani mai amfani da Instagram ya yi tsokaci a kan zancen inda ya ce, “Don Allah ko akwai wanda zai ba ni ruwan sha kofi daya, Nijeriya ta kusa sanya ni in suma! Ban da dukkan rancen kudin da ake karbowa, in ba a ce dabbobi ba, beraye da kwari sai kuma a ce … wai har yanzu biliyan na da ziro guda tara ne? Akwai bukatar mu #sakekarbarnaija #tsaftacenaija #sakeginanaija.”

ADVERTISEMENT

Wani kuma ya hau Tuwita ya yi tsokaci kamar haka: “Do Allah, ko akwai gwanayen lissafi a nan? Don Allah ku lissafa, ina so in ga nawa ne ake nufin APC ta kashe a kan wadannan matasan bogin su 177?
“Ya ku Matasa, kafin ku goyi bayan haukan nan da ake kira APC, ku tuna da wannan kanun labarin. In da an yi amfani da wannan kudin ta hanyar da ta dace, ai da mun samu matasa masu amfanarwa.”

Tabbaci: Jaridar PRNigeria ta lura da cewa wannan hoton ya na da tambarin ‘watermark’ “- 6mdh – photogrid” wanda ya sa ake ganin sa kamar tambarin jaridar PUNCH na gaske ne aka dauko daga masu amfani da soshiyal midiya daban-daban, saboda haka sai mu ka yi amfani da hikimar bincike ta ‘reberse image search’ a manhajar Google, a karshe sai sakamakon ya nuna mana cewa hoton wanda ya yi kama da na bangon gaba na mujalla babu inda ya fito a cikin shafukan zahiri na jaridar PUNCH da ke soshiyal midiya, kawai wasu masu amfani da shafukan zumunta ne su ka rika tura shi nan da can a Tuwita da Instagram.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Daga nan jaridar PRNigeria ta tuntubi sashen yada labarai na Ma’aikatar Harkokin Jinkai domin tabbatar da gaskiyar wannan magana, to amma sai wani jami’i da ya roki mu sakaya sunan sa ya bayyana lamarin da “Labarin bogi.”

Sai dai da PRNigeria ta gudanar da bincike kan wasu muhimman kalmomi a wurare daban-daban, ta gano cewa duk da yake hoton da aka yada karya ne, shi labarin ba karya ba ne amma kuma rahoto ne da ya fito watanni hudu da su ka gabata.
Gaskiya ne cewa Gwamnatin Tarayya ta bayyana a cikin Afrilu 2022 cewa ta ware kudi naira biliyan N5.9 domin horaswa da samar da kayan aiki da biyan alawus-alawus a kowane wata kan Rukunin C na shirin ‘N-Power’ a Jihar Kano, ba wai a kan matasa 177 kacal ba. Gwamnatin ta nanata cewa kimanin matasa 16,629 ne su ke amfana da shirin (karkashin Rukunin C) a jihar, ta kara da cewa a kiyasi har mutum 18,042 sun ci moriyar shirin a Rukunin A da na B na shirin.

Ministar Harkokin Jinkai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouk, ita ce ta ba da wannan bayanin ta hannun Mai Taimaka wa Shugaban Kasa na Musamman a Koyar da Sana’o’i, Dakta Nasir Mahmoud, lokacin da ya wakilce ta a wajen bikin yaye daliban shirin ‘N-Skills’, wanda wani sashe ne na ‘N-Power’, wanda aka yi a Kano, inda aka horas da matasa 177 kan gyaran waya.

Wannan bayanin ne jaridar PUNCH ta dauka ta lauya shi ta buga labarin da ya yaudari masu karatu, wanda tuni ta gyara labarin.

Kammalawa: Bisa ga shaidar da jaridar PRNigeria ta harhada, mun gano cewa ikirarin wai Gwamnatin Tarayya ta kashe naira biliyan 5.9 kan horas da matasa guda 177 su iya gyaran waya ba gaskiya ba ne. An fara buga rahoton a cikin jaridar PUNCH (shi ma ba a shafin farko ba) wanda tuni sun gyara shi tunda matasa 177 din da ake magana wani sashe ne kadai daga cikin jimillar matasa 16,629 da za a horas a Rukunin C na shirin ‘N-Power’ a Jihar Kano wadanda za su amfana da naira biliyan 5.9 da Gwamnatin Tarayya ta kasafta. Haka kuma, hoton da ake yadawa ba daga ita kan ta jaridar PUNCH ya fito ba, kawai wasu ne su ka kirkire shi domin su yaudari jama’a.

gwamnati
Musa Muhammad
+ postsBio
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    “Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ina Rokon Allah Ya Sa Na Kammala Sana’ar Fim Cikin Mutunci – Jarumi Sadik
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Atiku Ga ‘Yan Inugu: Za Mu Samar Muku Da Romon Dimokraɗiyya Idan Kuka Zaɓe Mu
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    2023: Atiku Ya Sha Alwashin Ƙara Wa Jihohi Da Ƙananan Hukumomi Ƙarfin Iko

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Dinkewar Kasar Sin Babbar Nasara Ce Ga Daukacin Duniya

Dinkewar Kasar Sin Babbar Nasara Ce Ga Daukacin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.