• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binani Ta Maka INEC A Kotu Kan Soke Ayyana Ta A Matsayin Wadda Ta Lashe Zaben Gwamnan Adamawa

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Binani Ta Maka INEC A Kotu Kan Soke Ayyana Ta  A Matsayin Wadda Ta Lashe Zaben Gwamnan Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aisha Dahiru, wadda aka fi sani da Binani, ‘yar takarar jam’iyyar APC a zaben gwamnan Adamawa, ta sake kai karar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Kamar yadda aka ruwaito a baya cewa INEC ta soke shelanta ta a matsayin gwamnan Adamawa a zaben gwamna da aka yi a ranar 18 ga Maris.

  • Abba Ya Sake Nada Sheikh Daurawa Shugaban Hisbah Ta Kano
  • Fisinjoji 20 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Hanyar Legas

Binani, wadda lauyanta, Michael Aondoaka, SAN, ya wakilta, ta gabatar da sabuwar kara a gaban mai shari’a Donatus Okorowo na babbar kotun tarayya da ke Abuja.

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/935/2023, ‘yar takarar jam’iyyar APC ta bayyana INEC, jam’iyyar PDP, da dan takararta, Gwamna Ahmadu Fintiri, a matsayin wadanda ta ke kara.

Binani na neman a binciki hukuncin da INEC ta yanke na sauya shelarta na farko a matsayin wadda ta lashe zaben da Kwamishinan Zabe na jihar, Hudu Yunusa-Ari ya yi.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

A yayin sauraren karar a ranar Litinin, Aondoaka ya bayar da hujjar cewa kotun sauraren kararrakin zabe ce ke da hurumin tantance makomar wadda yake karewa, inda ya ambaci sashe na 149 na dokar zabe na 2022.

Ya bayyana damuwarsa cewa matakin da INEC ta dauka zai hana Binani tanade-tanade da ke karkashin sashe na 285(6), wanda ya ba da damar kwanaki 180 don warware karar da ta shigar a gaban kotun a ranar 6 ga watan Mayu.

Aondoaka ya sanar da kotun cewa a baya an shigar da irin wannan kara a gaban mai shari’a Inyang Ekwo, wanda ya umarci Binani da ta garzaya kotun don wani lamari da ya shafi zabe.

Don haka, Aondoaka ya nemi a sake duba matakin na INEC kuma ya ba da wani aiki don nuna cewa karar da ake yi yanzu ba ta da tushe.

Ya tabbatar da cewa a shirye suke su biya duk wata tara idan har kotu ta ga cewa karar ba ta da tushe.

Mai shari’a Okorowo ya dage ci gaba da sauraren karar bayan ya saurari hujjojin Aondoaka.

Idan dai ba a manta ba Binani ta janye karar da ta shigar gaban mai shari’a Ekwo a ranar 26 ga watan Afrilu biyo bayan ayyana gwamna Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna.

Lauyan Binani, Mohammed Sheriff, ya gabatar da sanarwar dakatar da shi kuma ya bukaci kotu ta soke karar.

Sai dai mai shari’a Ekwo ya tunatar da Sheriff hukuncin da kotun ta bayar tun farko, inda ya bukaci ya yi magana ko kotu takori shari’ar.

Alkalin ya yanke shawarar yin watsi da batun, bayan da Sheriff ya kasa bi umarnin.

Ida tuna cewa da sanyin safiyar Lahadi, 16 ga Afrilu, 2023, ‘yan Nijeriya suka kadu da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Ahmed a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan jihar Adamawa da shugaban hukumar zaben jihar, Ari ya yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaAriBinaniFintiriINECKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’in Diflomasiyya Na Kasar Sin Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Gabon

Next Post

Ya Dace Amurka Ta Dauki Hakikanin Matakai Domin Karfafa Hadin Gwiwa Da Sin

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

6 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

20 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

22 hours ago
Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

24 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 day ago
Next Post
Ya Dace Amurka Ta Dauki Hakikanin Matakai Domin Karfafa Hadin Gwiwa Da Sin

Ya Dace Amurka Ta Dauki Hakikanin Matakai Domin Karfafa Hadin Gwiwa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.