• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binani Ta Maka INEC A Kotu Kan Soke Ayyana Ta A Matsayin Wadda Ta Lashe Zaben Gwamnan Adamawa

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Binani Ta Maka INEC A Kotu Kan Soke Ayyana Ta  A Matsayin Wadda Ta Lashe Zaben Gwamnan Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aisha Dahiru, wadda aka fi sani da Binani, ‘yar takarar jam’iyyar APC a zaben gwamnan Adamawa, ta sake kai karar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Kamar yadda aka ruwaito a baya cewa INEC ta soke shelanta ta a matsayin gwamnan Adamawa a zaben gwamna da aka yi a ranar 18 ga Maris.

  • Abba Ya Sake Nada Sheikh Daurawa Shugaban Hisbah Ta Kano
  • Fisinjoji 20 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Hanyar Legas

Binani, wadda lauyanta, Michael Aondoaka, SAN, ya wakilta, ta gabatar da sabuwar kara a gaban mai shari’a Donatus Okorowo na babbar kotun tarayya da ke Abuja.

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/935/2023, ‘yar takarar jam’iyyar APC ta bayyana INEC, jam’iyyar PDP, da dan takararta, Gwamna Ahmadu Fintiri, a matsayin wadanda ta ke kara.

Binani na neman a binciki hukuncin da INEC ta yanke na sauya shelarta na farko a matsayin wadda ta lashe zaben da Kwamishinan Zabe na jihar, Hudu Yunusa-Ari ya yi.

Labarai Masu Nasaba

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

A yayin sauraren karar a ranar Litinin, Aondoaka ya bayar da hujjar cewa kotun sauraren kararrakin zabe ce ke da hurumin tantance makomar wadda yake karewa, inda ya ambaci sashe na 149 na dokar zabe na 2022.

Ya bayyana damuwarsa cewa matakin da INEC ta dauka zai hana Binani tanade-tanade da ke karkashin sashe na 285(6), wanda ya ba da damar kwanaki 180 don warware karar da ta shigar a gaban kotun a ranar 6 ga watan Mayu.

Aondoaka ya sanar da kotun cewa a baya an shigar da irin wannan kara a gaban mai shari’a Inyang Ekwo, wanda ya umarci Binani da ta garzaya kotun don wani lamari da ya shafi zabe.

Don haka, Aondoaka ya nemi a sake duba matakin na INEC kuma ya ba da wani aiki don nuna cewa karar da ake yi yanzu ba ta da tushe.

Ya tabbatar da cewa a shirye suke su biya duk wata tara idan har kotu ta ga cewa karar ba ta da tushe.

Mai shari’a Okorowo ya dage ci gaba da sauraren karar bayan ya saurari hujjojin Aondoaka.

Idan dai ba a manta ba Binani ta janye karar da ta shigar gaban mai shari’a Ekwo a ranar 26 ga watan Afrilu biyo bayan ayyana gwamna Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna.

Lauyan Binani, Mohammed Sheriff, ya gabatar da sanarwar dakatar da shi kuma ya bukaci kotu ta soke karar.

Sai dai mai shari’a Ekwo ya tunatar da Sheriff hukuncin da kotun ta bayar tun farko, inda ya bukaci ya yi magana ko kotu takori shari’ar.

Alkalin ya yanke shawarar yin watsi da batun, bayan da Sheriff ya kasa bi umarnin.

Ida tuna cewa da sanyin safiyar Lahadi, 16 ga Afrilu, 2023, ‘yan Nijeriya suka kadu da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Ahmed a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan jihar Adamawa da shugaban hukumar zaben jihar, Ari ya yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaAriBinaniFintiriINECKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’in Diflomasiyya Na Kasar Sin Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Gabon

Next Post

Ya Dace Amurka Ta Dauki Hakikanin Matakai Domin Karfafa Hadin Gwiwa Da Sin

Related

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

22 seconds ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

5 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

9 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

10 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

1 day ago
Next Post
Ya Dace Amurka Ta Dauki Hakikanin Matakai Domin Karfafa Hadin Gwiwa Da Sin

Ya Dace Amurka Ta Dauki Hakikanin Matakai Domin Karfafa Hadin Gwiwa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.