• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Boko Haram Sun Kashe Limami Da Masallata 3 A Wani Hari Da Suka Kai Masallaci A Borno

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Sace Yara 3, Sun Bukaci Kudin Fansa Naira Miliyan 100 A Jihar Kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan ta’adda da ake kyautata zaton ‘yan Boko Haram ne, sun kashe wani babban limami da wasu masu ibada uku yayin da wasu da dama suka samu raunuka daban-daban a lokacin da ‘yan ta’addar suka kai hari a kauyen Ngulde da ke karamar hukumar Askira-Uba a jihar Borno.

LEADERSHIP ta rawaito cewa ‘yan ta’addar wadanda yawansu ya kai 20, sun kaddamar da harin ne a ranar Juma’a, inda suka bude wuta kan masallatan bayan sun idar da sallar Fajir a masallacin.

  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Masunta A Tafkin Chadi
  • An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

Rahotanni sun ce ‘yan ta’addar sun yi awon gaba da dabbobi da kayan abinci tare da kona motoci biyu a yankin Ngulde da ke wani yanki na dajin Sambisa a jihar.

Da yake tsokaci kan harin, Kansila mai wakiltar Ngulde Ward a karamar hukumar Askira-Uba, Hon. Bilyaminu Umar, ya mika sakon ta’aziyya da jajantawa ga daukacin al’ummar mazabarsa kan harin da mayakan Boko Haram suka kai musu, wanda ya afku a ranar 2 ga Satumba, 2022.

Ya ce, “Mazabar Ngulde na daya daga cikin mazabun da al’ummar karamar hukumar Askira-Uba suka ba ni izinin wakiltarsu a zaben kananan hukumomin da ya gabata. Tun daga wannan lokacin, ina jin daɗin haɗin kai da goyon bayansu. Don haka, na ji matukar kaduwa da jin bakin cikin wannan sabon hari, lokacin da yawancin mutanena suka shagaltu da yin amfani da lokacin noman bana.

Labarai Masu Nasaba

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

“Harin wanda ya faru da sanyin safiyar Juma’a, 2 ga watan Satumba, 2022, bayan sallar Fajir, ya yi sanadin mutuwar mutane hudu (4) tare da jikkata wasu da dama, yayin da kuma wasu ‘yan bindiga suka lalata dukiyoyi da wuraren kasuwanci na miliyoyin naira da tayar da kayar baya.

“Tuni na sanar da mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Borno, Hon. Engr Abdullahi Askira, akan kai harin na rashin tausayi. Ya yi alkawarin isar da shi ga Gwamnan Jihar, Farfesa Babagana Umara Zulum, domin daukar matakin da ya dace.”

Da aka tuntubi mataimakin kakakin majalisar jihar Borno, wanda kuma ke wakiltar mazabar Askira-Uba, Abdullahi Askira, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce, “Eh, na samu kiran waya jiya cewa wasu ‘yan ta’adda sun kai farmaki garin Ngulde inda suka kashe mutane uku nan take, yayin da wani mutum daya kuma ya rasu a hanyar zuwa asibitin Garkida inda aka garzaya da wadanda suka jikkata domin yi musu magani.

“Masu tayar da kayar bayan sun kai kimanin 20, sun mamaye al’ummar ne da misalin karfe 6:30 na safe, inda suka nemi a nuna musu wuri ko gidan shugaban mafarauta/’yan banga.

“Ba tare da bata lokaci ba, kai tsaye suka je wajen wasu masallata da suka kammala Sallar Fajir a Masallaci suka bude wuta, lamarin da ya kai ga kashe mutane uku nan take, ciki har da babban limamin sashin Gima.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Wata-ga-wata: Gwamnati Ta Sake Bankado Kadarorin Abba Kyari

Next Post

NDLEA Ta Cafke Wani Mai Nakasa Da Ke Safaran Miyagun Kwayoyi Da Tulin Wiwi Da Wasu Kwayoyi

Related

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

4 minutes ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

2 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

4 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

6 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

8 hours ago
Next Post
NDLEA Ta Cafke Wani Mai Nakasa Da Ke Safaran Miyagun Kwayoyi Da Tulin Wiwi Da Wasu Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Wani Mai Nakasa Da Ke Safaran Miyagun Kwayoyi Da Tulin Wiwi Da Wasu Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.