ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Boko Haram Sun Kashe Limami Da Masallata 3 A Wani Hari Da Suka Kai Masallaci A Borno

by Muhammad
4 years ago
Boko

Wasu ‘yan ta’adda da ake kyautata zaton ‘yan Boko Haram ne, sun kashe wani babban limami da wasu masu ibada uku yayin da wasu da dama suka samu raunuka daban-daban a lokacin da ‘yan ta’addar suka kai hari a kauyen Ngulde da ke karamar hukumar Askira-Uba a jihar Borno.

LEADERSHIP ta rawaito cewa ‘yan ta’addar wadanda yawansu ya kai 20, sun kaddamar da harin ne a ranar Juma’a, inda suka bude wuta kan masallatan bayan sun idar da sallar Fajir a masallacin.

  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Masunta A Tafkin Chadi
  • An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

Rahotanni sun ce ‘yan ta’addar sun yi awon gaba da dabbobi da kayan abinci tare da kona motoci biyu a yankin Ngulde da ke wani yanki na dajin Sambisa a jihar.

ADVERTISEMENT

Da yake tsokaci kan harin, Kansila mai wakiltar Ngulde Ward a karamar hukumar Askira-Uba, Hon. Bilyaminu Umar, ya mika sakon ta’aziyya da jajantawa ga daukacin al’ummar mazabarsa kan harin da mayakan Boko Haram suka kai musu, wanda ya afku a ranar 2 ga Satumba, 2022.

Ya ce, “Mazabar Ngulde na daya daga cikin mazabun da al’ummar karamar hukumar Askira-Uba suka ba ni izinin wakiltarsu a zaben kananan hukumomin da ya gabata. Tun daga wannan lokacin, ina jin daɗin haɗin kai da goyon bayansu. Don haka, na ji matukar kaduwa da jin bakin cikin wannan sabon hari, lokacin da yawancin mutanena suka shagaltu da yin amfani da lokacin noman bana.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

“Harin wanda ya faru da sanyin safiyar Juma’a, 2 ga watan Satumba, 2022, bayan sallar Fajir, ya yi sanadin mutuwar mutane hudu (4) tare da jikkata wasu da dama, yayin da kuma wasu ‘yan bindiga suka lalata dukiyoyi da wuraren kasuwanci na miliyoyin naira da tayar da kayar baya.

“Tuni na sanar da mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Borno, Hon. Engr Abdullahi Askira, akan kai harin na rashin tausayi. Ya yi alkawarin isar da shi ga Gwamnan Jihar, Farfesa Babagana Umara Zulum, domin daukar matakin da ya dace.”

Da aka tuntubi mataimakin kakakin majalisar jihar Borno, wanda kuma ke wakiltar mazabar Askira-Uba, Abdullahi Askira, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce, “Eh, na samu kiran waya jiya cewa wasu ‘yan ta’adda sun kai farmaki garin Ngulde inda suka kashe mutane uku nan take, yayin da wani mutum daya kuma ya rasu a hanyar zuwa asibitin Garkida inda aka garzaya da wadanda suka jikkata domin yi musu magani.

“Masu tayar da kayar bayan sun kai kimanin 20, sun mamaye al’ummar ne da misalin karfe 6:30 na safe, inda suka nemi a nuna musu wuri ko gidan shugaban mafarauta/’yan banga.

“Ba tare da bata lokaci ba, kai tsaye suka je wajen wasu masallata da suka kammala Sallar Fajir a Masallaci suka bude wuta, lamarin da ya kai ga kashe mutane uku nan take, ciki har da babban limamin sashin Gima.”

Boko
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Wani Mai Nakasa Da Ke Safaran Miyagun Kwayoyi Da Tulin Wiwi Da Wasu Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Wani Mai Nakasa Da Ke Safaran Miyagun Kwayoyi Da Tulin Wiwi Da Wasu Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.