ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Boko Haram Sun Kashe Limami Da Masallata 3 A Wani Hari Da Suka Kai Masallaci A Borno

by Muhammad
4 years ago
Boko

Wasu ‘yan ta’adda da ake kyautata zaton ‘yan Boko Haram ne, sun kashe wani babban limami da wasu masu ibada uku yayin da wasu da dama suka samu raunuka daban-daban a lokacin da ‘yan ta’addar suka kai hari a kauyen Ngulde da ke karamar hukumar Askira-Uba a jihar Borno.

LEADERSHIP ta rawaito cewa ‘yan ta’addar wadanda yawansu ya kai 20, sun kaddamar da harin ne a ranar Juma’a, inda suka bude wuta kan masallatan bayan sun idar da sallar Fajir a masallacin.

  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Masunta A Tafkin Chadi
  • An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

Rahotanni sun ce ‘yan ta’addar sun yi awon gaba da dabbobi da kayan abinci tare da kona motoci biyu a yankin Ngulde da ke wani yanki na dajin Sambisa a jihar.

ADVERTISEMENT

Da yake tsokaci kan harin, Kansila mai wakiltar Ngulde Ward a karamar hukumar Askira-Uba, Hon. Bilyaminu Umar, ya mika sakon ta’aziyya da jajantawa ga daukacin al’ummar mazabarsa kan harin da mayakan Boko Haram suka kai musu, wanda ya afku a ranar 2 ga Satumba, 2022.

Ya ce, “Mazabar Ngulde na daya daga cikin mazabun da al’ummar karamar hukumar Askira-Uba suka ba ni izinin wakiltarsu a zaben kananan hukumomin da ya gabata. Tun daga wannan lokacin, ina jin daɗin haɗin kai da goyon bayansu. Don haka, na ji matukar kaduwa da jin bakin cikin wannan sabon hari, lokacin da yawancin mutanena suka shagaltu da yin amfani da lokacin noman bana.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Harin wanda ya faru da sanyin safiyar Juma’a, 2 ga watan Satumba, 2022, bayan sallar Fajir, ya yi sanadin mutuwar mutane hudu (4) tare da jikkata wasu da dama, yayin da kuma wasu ‘yan bindiga suka lalata dukiyoyi da wuraren kasuwanci na miliyoyin naira da tayar da kayar baya.

“Tuni na sanar da mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Borno, Hon. Engr Abdullahi Askira, akan kai harin na rashin tausayi. Ya yi alkawarin isar da shi ga Gwamnan Jihar, Farfesa Babagana Umara Zulum, domin daukar matakin da ya dace.”

Da aka tuntubi mataimakin kakakin majalisar jihar Borno, wanda kuma ke wakiltar mazabar Askira-Uba, Abdullahi Askira, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce, “Eh, na samu kiran waya jiya cewa wasu ‘yan ta’adda sun kai farmaki garin Ngulde inda suka kashe mutane uku nan take, yayin da wani mutum daya kuma ya rasu a hanyar zuwa asibitin Garkida inda aka garzaya da wadanda suka jikkata domin yi musu magani.

“Masu tayar da kayar bayan sun kai kimanin 20, sun mamaye al’ummar ne da misalin karfe 6:30 na safe, inda suka nemi a nuna musu wuri ko gidan shugaban mafarauta/’yan banga.

“Ba tare da bata lokaci ba, kai tsaye suka je wajen wasu masallata da suka kammala Sallar Fajir a Masallaci suka bude wuta, lamarin da ya kai ga kashe mutane uku nan take, ciki har da babban limamin sashin Gima.”

Boko
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Wani Mai Nakasa Da Ke Safaran Miyagun Kwayoyi Da Tulin Wiwi Da Wasu Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Wani Mai Nakasa Da Ke Safaran Miyagun Kwayoyi Da Tulin Wiwi Da Wasu Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.