• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ne Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Kangin Talauci — Gwamnoni

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Buhari Ne Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Kangin Talauci — Gwamnoni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnonin Nijeriya 36 sun shaida wa shugaban kasa Muhammadu Buhari, cewar gazawarsa wajen samar da tsaro da kuma kasa cika alkawuran da ya daukar wa ‘yan Nijeriya ne dalilan da suka jefa jama’ar kasar nan cikin halin kunci rayuwa da talauci.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnonin, Abdurazaque Bello-Barkindo, ya rabawa manema labarai, ta ce abin takaici ne yaddda gwamnatin tarayya ke neman dora wa gwamnonin laifi dangane da irin talauci da halin kuncin da mazauna yankunan karkarar kasar nan ke fama da su.

  • Sinawa Na Jimamin Rasuwar Jiang Zemin
  • Alkalai 15 Za Su Gurfana Gaban NJC Kan Zargin Aikata Rashin Da’a

Gwamnonin sun ce a 2019, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin cewar zai fitar da mutane miliyan 100 daga kangin talaucin da ya addabi jama’a, amma a yau alkaluma sun nuna cewar ‘yan Nijeriya sama da miliyan 130 ne ke fama da talauci, inda suke rayuwa kasa da Dala guda a kowace rana.

Sanarwar ta ce a karkashin gwamnatin Buhari, an kwashe watanni kamfanin man NNPC ba ya iya zuba ribar da yake samu a asusun gwamnati, abin da ya tilasta wa gwamnonin neman mafita ta wasu hanyoyi wajen samun kudaden shiga domin cike gibin kudaden da suke samu daga gwamnatin tarayya domin sauke nauyin da ke kansu a bangare noma da raya karkara da ayyukan jinkai da kuma kula da lafiyar jama’a.

Gwamnonin sun kuma caccaki ministan kasafin kudi, Clement Agba, wanda ya zargi gwamnonin da jefa mutane sama da kashi 72 a yankunan karkara cikin talauci da shara karya wajen kauda kan jama’a daga assalin abin da yake faruwa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

Sanarwar ta ce abin sani shi ne, aikin farko da ya rataya a kan gwamnatin tarayya, shi ne kare lafiya da kuma dukiyoyin jama’a wajen samar da tsaro, domin aiwatar da harkokin ci gaba, amma abin takaici gwamnatin tarayya ta gaza a wannan bangaren, inda ta bar ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda da kuma masu garkuwa da mutane suka mayar da kasar dandalin kashe jama’a da sace mutane a gidajensu da makarantu da kasuwanni da kuma gonaki.

Gwamnonin sun ce tabbas gazawar shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke jagorancin gwamnatin tarayya, ne ya haifar da dalilan kasa noma da samar da abinci da kuma harkokin kasuwaci a yankunan karkara, saboda yadda zaman lafiya ya gagara, abin da ya hana mutane zuwa gonakinsu da kuma kasuwanni.

Wannan martini na zuwa ne ya biyo bayan zargin da ministan kasafin kudi, Clement Agba, ya yi wa gwamnonin, inda ce sun mayar da hankali wajen gina gadodin sama da filayen jiragen sama, maimakon bunkasa rayuwar jama’ar karkara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlkawariBuhariGwamnoniKarkaraMartaniNNPCTalauci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sinawa Na Jimamin Rasuwar Jiang Zemin

Next Post

Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

Related

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

5 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

13 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

15 hours ago
Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul
Manyan Labarai

Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

18 hours ago
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

1 day ago
Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

1 day ago
Next Post
Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.