ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Cika Alkawarin Da Ya Dauka Game Da Zaben 2023 -Gwamnatin Tarayya

by Sadiq
3 years ago
Buhari

Gwamnatin Tarayya ta ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ya cika alkawarin da ya dauka na gudanar da sahihin zaben a 2023.

Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya bayyana hakan a birnin Washington DC a lokacin da yake ganawa da wasu kungiyoyin yada labarai na duniya.

  • An Kama Mutane 3 Kan Zarginsu Da Hannu A Kisan Wasu 2 A Kaduna
  • Gwamnatin Kano Ta Nada Jega A Matsayin Shugaban Jami’ar Sa’adatu Rimi

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya ruwaito cewa ministan ya je Washington ne domin tattaunawa da kungiyoyin yada labarai na kasa da kasa da masu tunani kan zaben 2023 da aka kammala.

ADVERTISEMENT

NAN ta kuma ruwaito cewa kawo yanzu ministan ya yi gana da “Washington Post”, Muryar Amurka, Associated Press da Mujallar manufofin kasashen waje.

Ministan ya ce Buhari ya cika alkawarin da ya yi na dawo da sahihin zabe, ya yanke shawarar cewa ba zai bai wa wata jam’iyyar siyasa dama ta musamman ba, ciki har da jam’iyyar APC mai mulki a lokacin zaben.

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Ya ce a lokacin zabukan da suka gabata, shugaban kasar ya tabbatar da cewa babu wanda ya yi amfani da jami’an tsaro wajen magudin zabe amma ya samar da daidaito wajen gudanar da zaben.

“Misalin wannan alkawari, shi ne jam’iyyar shugaban kasa ta fadi zaben shugaban kasa a Katsina, jiharsa ta haihuwa.

“Haka zalika, zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, ya sha kaye a jiharsa ta Legas, yayin da shugaban jam’iyyar, Abdulahi Adamu, ya sha kaye a jihar Nasarawa a hannun jam’iyyar LP.

“Shugaban kungiyar yakin neman zaben jam’iyyarmu ma ya sha kaye a hannun PDP a Jihar Filato.

“Babu wani abu da ya ba wannan zaben ya koyar face gaskiya fiye, saboda babu wani magudi a jihohinmu,” in ji shi.

Ministan ya kara da cewa jam’iyyar APC ta sha kaye a jihohi hudu da suka fi yawan kuri’u a zabuka – Katsina, Kano, Kaduna da kuma Legas ko a lokacin da jam’iyyar ke rike da madafun iko.

Mohammed, ya ce zarge-zargen da ake yi na zamba da ‘yan adawa da masu zanga-zangar suka yi, bai taka kara ya karya ba.

A cewar ministan, rikicin ya samo asali ne saboda gazawar hukumar zabe ta INEC wajen dora sakamakon zaben shugaban kasa na ainihi a kan lokacin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
Mu Za Mu Yi Nasara A Kotu —Kashuri

Mu Za Mu Yi Nasara A Kotu —Kashuri

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.