ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Cika Alkawarin Da Ya Dauka Game Da Zaben 2023 -Gwamnatin Tarayya

by Sadiq
3 years ago
Buhari

Gwamnatin Tarayya ta ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ya cika alkawarin da ya dauka na gudanar da sahihin zaben a 2023.

Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya bayyana hakan a birnin Washington DC a lokacin da yake ganawa da wasu kungiyoyin yada labarai na duniya.

  • An Kama Mutane 3 Kan Zarginsu Da Hannu A Kisan Wasu 2 A Kaduna
  • Gwamnatin Kano Ta Nada Jega A Matsayin Shugaban Jami’ar Sa’adatu Rimi

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya ruwaito cewa ministan ya je Washington ne domin tattaunawa da kungiyoyin yada labarai na kasa da kasa da masu tunani kan zaben 2023 da aka kammala.

ADVERTISEMENT

NAN ta kuma ruwaito cewa kawo yanzu ministan ya yi gana da “Washington Post”, Muryar Amurka, Associated Press da Mujallar manufofin kasashen waje.

Ministan ya ce Buhari ya cika alkawarin da ya yi na dawo da sahihin zabe, ya yanke shawarar cewa ba zai bai wa wata jam’iyyar siyasa dama ta musamman ba, ciki har da jam’iyyar APC mai mulki a lokacin zaben.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ya ce a lokacin zabukan da suka gabata, shugaban kasar ya tabbatar da cewa babu wanda ya yi amfani da jami’an tsaro wajen magudin zabe amma ya samar da daidaito wajen gudanar da zaben.

“Misalin wannan alkawari, shi ne jam’iyyar shugaban kasa ta fadi zaben shugaban kasa a Katsina, jiharsa ta haihuwa.

“Haka zalika, zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, ya sha kaye a jiharsa ta Legas, yayin da shugaban jam’iyyar, Abdulahi Adamu, ya sha kaye a jihar Nasarawa a hannun jam’iyyar LP.

“Shugaban kungiyar yakin neman zaben jam’iyyarmu ma ya sha kaye a hannun PDP a Jihar Filato.

“Babu wani abu da ya ba wannan zaben ya koyar face gaskiya fiye, saboda babu wani magudi a jihohinmu,” in ji shi.

Ministan ya kara da cewa jam’iyyar APC ta sha kaye a jihohi hudu da suka fi yawan kuri’u a zabuka – Katsina, Kano, Kaduna da kuma Legas ko a lokacin da jam’iyyar ke rike da madafun iko.

Mohammed, ya ce zarge-zargen da ake yi na zamba da ‘yan adawa da masu zanga-zangar suka yi, bai taka kara ya karya ba.

A cewar ministan, rikicin ya samo asali ne saboda gazawar hukumar zabe ta INEC wajen dora sakamakon zaben shugaban kasa na ainihi a kan lokacin.

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Mu Za Mu Yi Nasara A Kotu —Kashuri

Mu Za Mu Yi Nasara A Kotu —Kashuri

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.