ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Cika Alkawarin Da Ya Dauka Game Da Zaben 2023 -Gwamnatin Tarayya

by Sadiq
3 years ago
Buhari

Gwamnatin Tarayya ta ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ya cika alkawarin da ya dauka na gudanar da sahihin zaben a 2023.

Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya bayyana hakan a birnin Washington DC a lokacin da yake ganawa da wasu kungiyoyin yada labarai na duniya.

  • An Kama Mutane 3 Kan Zarginsu Da Hannu A Kisan Wasu 2 A Kaduna
  • Gwamnatin Kano Ta Nada Jega A Matsayin Shugaban Jami’ar Sa’adatu Rimi

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya ruwaito cewa ministan ya je Washington ne domin tattaunawa da kungiyoyin yada labarai na kasa da kasa da masu tunani kan zaben 2023 da aka kammala.

ADVERTISEMENT

NAN ta kuma ruwaito cewa kawo yanzu ministan ya yi gana da “Washington Post”, Muryar Amurka, Associated Press da Mujallar manufofin kasashen waje.

Ministan ya ce Buhari ya cika alkawarin da ya yi na dawo da sahihin zabe, ya yanke shawarar cewa ba zai bai wa wata jam’iyyar siyasa dama ta musamman ba, ciki har da jam’iyyar APC mai mulki a lokacin zaben.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ya ce a lokacin zabukan da suka gabata, shugaban kasar ya tabbatar da cewa babu wanda ya yi amfani da jami’an tsaro wajen magudin zabe amma ya samar da daidaito wajen gudanar da zaben.

“Misalin wannan alkawari, shi ne jam’iyyar shugaban kasa ta fadi zaben shugaban kasa a Katsina, jiharsa ta haihuwa.

“Haka zalika, zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, ya sha kaye a jiharsa ta Legas, yayin da shugaban jam’iyyar, Abdulahi Adamu, ya sha kaye a jihar Nasarawa a hannun jam’iyyar LP.

“Shugaban kungiyar yakin neman zaben jam’iyyarmu ma ya sha kaye a hannun PDP a Jihar Filato.

“Babu wani abu da ya ba wannan zaben ya koyar face gaskiya fiye, saboda babu wani magudi a jihohinmu,” in ji shi.

Ministan ya kara da cewa jam’iyyar APC ta sha kaye a jihohi hudu da suka fi yawan kuri’u a zabuka – Katsina, Kano, Kaduna da kuma Legas ko a lokacin da jam’iyyar ke rike da madafun iko.

Mohammed, ya ce zarge-zargen da ake yi na zamba da ‘yan adawa da masu zanga-zangar suka yi, bai taka kara ya karya ba.

A cewar ministan, rikicin ya samo asali ne saboda gazawar hukumar zabe ta INEC wajen dora sakamakon zaben shugaban kasa na ainihi a kan lokacin.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Mu Za Mu Yi Nasara A Kotu —Kashuri

Mu Za Mu Yi Nasara A Kotu —Kashuri

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.