ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Ta Nada Jega A Matsayin Shugaban Jami’ar Sa’adatu Rimi

by Sadiq
3 years ago
Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nada tsohon shugaban hukumar zabe ta kasa (INEC), Farfesa Muhammad Attahiru Jega a matsayin uba ga sabuwar Jami’ar nazarin koyar da aikin malinta ta Kano, Kumbotso.

Kazalika Gwamnatin ta Kano, ta amince da nada Oba Dokta Moshood Olalekan Ishola Balogun Aliiwo a matsayin shugaban majalisar kula da ayyukan Jami’ar.

  • Matasa Sun Kashe Dan Sanda Garin Rabon Fada A Neja
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Adamawa

Gabanin zama shugaban INEC, Farfesa Attahiru Jega ya shugabanci Jami’ar Bayero Kano tsawon shekaru biyar, haka kuma kafin haka, ya kwashe shekaru da dama yana koyar da ilimin kimiyyar siyasa a Jami’ar ta Bayero.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan labaran gwamnatin Kano, Malam Mohammed Garba wanda ya sanar da haka bayan zaman majalisar zartarwa ta jihar da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranta a ranar Lahadi, ya ce a kwanan nan ne hukumar kula da Jami’o’i ta Nijeriya wato NUC ta amince da daga likafar kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi zuwa matsayin Jami’ar nazarin koyon aikin malinta.

Kwamishinan ya ce sauran mambobin majalisar kula da ayyukan sabuwar Jami’ar sun hada da Dokta Muhammad Adamu Kwankwaso da Hajiya Zulaiha U.M Ahmed da Dokta Ibrahim Yakubu Wunti Dokta Halima Muhammad da kuma Alhaji Sabiu Bako.

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

A cewar Kwamishinan, Mlmajalisar zartarwar ta Kano ta amince da nada shugabannin da zasu tafiyar da ayyukan Jami’ar na yau da kullum, wadanda suka hada da Farfesa Isa Yahaya Bunkure a matsayin shugaban Jami’ar da Kabiru Ahmed Gwarzo mataimakin shugaba mai kula da al’amuran karatu da Doktw Miswaru Bello mataimakin shugaba mai kula da harkokin mulki sai kuma Saminu Bello babban magatakarda na Jami’ar.

Sauran su ne Hajiya Mabruka Abubakar Abba shugabar sashin kula da dakunan karatu na Jami’ar yayin da aka nada Ibrahim Muhammad Yahaya babban jami’in kula da al’amuran kudade.

Ita dai sabuwar Jami’ar nazari da koyon aikin malinta ta Sa’adatu Rimi da ke Kano, ita ce ta 61 a jerin Jami’o’i mallakar jihohi yayin da ta kasance ta 222 a jerin Jami’o’in Nijeriya.

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Next Post
An Kama Mutane 3 Kan Zarginsu Da Hannu A Kisan Wasu 2 A Kaduna

An Kama Mutane 3 Kan Zarginsu Da Hannu A Kisan Wasu 2 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.