• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Muhammadu Buhari ya kafa hukumar gudanarwa ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC) mai wakilai goma sha biyu da su ka haɗa da Daraktan Sashen Harkokin Jinƙai a Ma’aikatar Harkokin Jinƙai Agaji da Inganta Rayuwa ta Tarayya, Alhaji Grema Ali.

 

A sanarwar da mai ba ministar harkokin jinƙai shawara kan aikin jarida, Nneka Ikem Anibeze, ta raba a Abuja a ranar Litinin, an bayyana cewa Buhari ya aika da takarda zuwa ga Shugaban Majalisar Dattawa Ahmed Lawan a ranar 3 ga Mayu, 2023, inda ya buƙaci majalisar da ta amince da naɗin sababbin membobin hukumar gudanarwar.

  • Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku

Shugaban ƙasar ya ce: ‘‘Kamar yadda Sashe na 1, ƙaramin sashe na 2(5)(b) na Dokar Kafa Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas ta 2017 ya tanadar, ina farin cikin gabatar wa da Majalisar Dattawa mutum 12 da aka zaɓa, kamar yadda aka jero su a nan ƙasa, a matsayin membobin Hukumar Gudanarwa ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

‘‘Ina kira ga Majalisar Dattawa da ta lura da cewa wa’adin ‘yan Hukumar Gudanarwar Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas zai ƙare a ranar 7 ga Mayu, 2023.’’

 

Waɗanda aka zaɓa ɗin dai su ne: Lauya Bashir Bukar Baale, Ciyaman (Arewa-maso-gabas, Yobe), Suwaiba Idris Baba, Babbar Darakta, Harkokin Jinƙai (Arewa-maso-gabas, Taraba), Musa Umar Yashi, Babban Daraktan Gudanarwa da Kuɗi (Arewa-maso-gabas, Bauchi), Dakta Isma’ila Nuhu Maksha, Babban Daraktan Ayyuka (Arewa-maso-gabas, Adamawa), da Umar Abubakar Hashidu, Shugaba (Arewa-maso-gabas, Gombe).

 

Sauran su ne Grema Ali, memba (Arewa-maso-gabas, Borno), Onyeka Gospel-Tony, memba (Kudu-maso-gabas), Hon. Madam Hailmary Ogolo Aipoh, memba (Kudu-maso-kudu), Air Commodore Babatunde Akanbi (ritaya), memba (Kudu-maso-yamma), Mustapha Ahmed Ibrahim, memba (Arewa-maso-yamma), Hadiza Maina, memba (Arewa ta Tsakiya), da wakili daga Ma’aikatar Kuɗi, Kasafi da Tsare-tsaren Ƙasa ta Tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fintiri Ya Rantsar Da Mace Ta Farko Babbar Mai Shari’a A Adamawa

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sako Karin Dalibai 3 Na Kwalejin Jihar Kebbi

Related

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

7 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

9 hours ago
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
Labarai

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

10 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

12 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

12 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

15 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sako Karin Dalibai 3 Na Kwalejin Jihar Kebbi

'Yan Bindiga Sun Sako Karin Dalibai 3 Na Kwalejin Jihar Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.