• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Musanta Hana Tinubu Binciken Tsofaffin Jami’an Gwamnatinsa 

by Abubakar Abba
2 years ago
Buhari

Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi kakkausar suka dangane da wani ikirari da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke nuna cewa ya bukaci magajinsa, Bola Ahmed Tinubu da ya daina binciken wasu tsoffin jami’an gwamnatinsa.

Da yake bayyana rahotannin a matsayin “labaran karya,” mai magana da yawun Buhari, Garba Shehu, a wata sanarwa da ya fitar, ya bukaci jama’a da kada su amince da irin wadannan bayanai marasa tushe.

  • Mataimakin Shugaban Kungiyar Miyetti Allah Ya Bace
  • NLC Za Ta Yi Zama Kan Hana Wasu Ma’aikatan Kano Albashi

A cewar Shehu, da gan-gan Buhari ya zabi ya ci mutuncinsa da kuma kaucewa jawo hankalinsa domin kaucewa duk wani abu da zai kawo wa sabuwar gwamnati cikas.

Da yake neman zaman kadaici, ya ce tun da farko tsohon shugaban ya koma mahaifarsa ta Daura amma ya ga an gagara samun kwanciyar hankali da ake bukata saboda yawan masu ziyara.

Sakamakon haka, Shehu ya ce tsohon shugaban ya koma wani wurin da aka kebe, inda yake fatan samun hutun da ya ke nema.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Shehu ya nanata muhimmancin yin watsi da wadannan ikirari marasa tushe, inda ya jaddada bukatar mayar da hankali kan bayanai na gaskiya da tabbatar da gaskiya.

A cewarsa, babban abin da tsohon shugaban kasar ya sa a gaba shi ne zaman lafiyarsa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu za ta yi aiki yadda ya kamata wajen cika alkawurran zaben da suka yi.

Ya ce “Idan za a yi imani da kafafen sadarwa na zamani, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari yana rokon magajinsa, Bola Ahmed Tinubu da kada ya binciki wasu tsoffin jami’an gwamnatinsa.

“Karya ne, ba a tattauna wani abu makamacin haka ba. Wannan labarin karya ne, kuma ba wani abu ba. Alhamdulillahi ba kowa a dakin da suka hadu sai shugabannin biyu, don haka babu wanda ya isa ya kawo labarin tattaunawar tasu.

Duk mai yiwuwa, tsohon shugaban kasar yana fatan ya kasance a waje da abin da ya faru don kada ya dauke hankalin sabuwar gwamnati.

“Ya zabi ya koma gida Daura da fatan ya samu hutu ya kuma bai wa gwamnatin damar yin aikinta.

Ya ci gaba da cewa, “Ba abin da yake fatan samu face hutu, kuma gwamnatin Tinubu ta samu yanayi mai kyau na yin aiki kan cika alkawuran da suka dauka.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Next Post
Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

LABARAI MASU NASABA

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.