• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Musanta Hana Tinubu Binciken Tsofaffin Jami’an Gwamnatinsa 

by Abubakar Abba
2 years ago
Buhari

Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi kakkausar suka dangane da wani ikirari da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke nuna cewa ya bukaci magajinsa, Bola Ahmed Tinubu da ya daina binciken wasu tsoffin jami’an gwamnatinsa.

Da yake bayyana rahotannin a matsayin “labaran karya,” mai magana da yawun Buhari, Garba Shehu, a wata sanarwa da ya fitar, ya bukaci jama’a da kada su amince da irin wadannan bayanai marasa tushe.

  • Mataimakin Shugaban Kungiyar Miyetti Allah Ya Bace
  • NLC Za Ta Yi Zama Kan Hana Wasu Ma’aikatan Kano Albashi

A cewar Shehu, da gan-gan Buhari ya zabi ya ci mutuncinsa da kuma kaucewa jawo hankalinsa domin kaucewa duk wani abu da zai kawo wa sabuwar gwamnati cikas.

Da yake neman zaman kadaici, ya ce tun da farko tsohon shugaban ya koma mahaifarsa ta Daura amma ya ga an gagara samun kwanciyar hankali da ake bukata saboda yawan masu ziyara.

Sakamakon haka, Shehu ya ce tsohon shugaban ya koma wani wurin da aka kebe, inda yake fatan samun hutun da ya ke nema.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Shehu ya nanata muhimmancin yin watsi da wadannan ikirari marasa tushe, inda ya jaddada bukatar mayar da hankali kan bayanai na gaskiya da tabbatar da gaskiya.

A cewarsa, babban abin da tsohon shugaban kasar ya sa a gaba shi ne zaman lafiyarsa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu za ta yi aiki yadda ya kamata wajen cika alkawurran zaben da suka yi.

Ya ce “Idan za a yi imani da kafafen sadarwa na zamani, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari yana rokon magajinsa, Bola Ahmed Tinubu da kada ya binciki wasu tsoffin jami’an gwamnatinsa.

“Karya ne, ba a tattauna wani abu makamacin haka ba. Wannan labarin karya ne, kuma ba wani abu ba. Alhamdulillahi ba kowa a dakin da suka hadu sai shugabannin biyu, don haka babu wanda ya isa ya kawo labarin tattaunawar tasu.

Duk mai yiwuwa, tsohon shugaban kasar yana fatan ya kasance a waje da abin da ya faru don kada ya dauke hankalin sabuwar gwamnati.

“Ya zabi ya koma gida Daura da fatan ya samu hutu ya kuma bai wa gwamnatin damar yin aikinta.

Ya ci gaba da cewa, “Ba abin da yake fatan samu face hutu, kuma gwamnatin Tinubu ta samu yanayi mai kyau na yin aiki kan cika alkawuran da suka dauka.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.