ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Musanta Hana Tinubu Binciken Tsofaffin Jami’an Gwamnatinsa 

by Abubakar Abba
3 years ago
Buhari

Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi kakkausar suka dangane da wani ikirari da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke nuna cewa ya bukaci magajinsa, Bola Ahmed Tinubu da ya daina binciken wasu tsoffin jami’an gwamnatinsa.

Da yake bayyana rahotannin a matsayin “labaran karya,” mai magana da yawun Buhari, Garba Shehu, a wata sanarwa da ya fitar, ya bukaci jama’a da kada su amince da irin wadannan bayanai marasa tushe.

  • Mataimakin Shugaban Kungiyar Miyetti Allah Ya Bace
  • NLC Za Ta Yi Zama Kan Hana Wasu Ma’aikatan Kano Albashi

A cewar Shehu, da gan-gan Buhari ya zabi ya ci mutuncinsa da kuma kaucewa jawo hankalinsa domin kaucewa duk wani abu da zai kawo wa sabuwar gwamnati cikas.

ADVERTISEMENT

Da yake neman zaman kadaici, ya ce tun da farko tsohon shugaban ya koma mahaifarsa ta Daura amma ya ga an gagara samun kwanciyar hankali da ake bukata saboda yawan masu ziyara.

Sakamakon haka, Shehu ya ce tsohon shugaban ya koma wani wurin da aka kebe, inda yake fatan samun hutun da ya ke nema.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Shehu ya nanata muhimmancin yin watsi da wadannan ikirari marasa tushe, inda ya jaddada bukatar mayar da hankali kan bayanai na gaskiya da tabbatar da gaskiya.

A cewarsa, babban abin da tsohon shugaban kasar ya sa a gaba shi ne zaman lafiyarsa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu za ta yi aiki yadda ya kamata wajen cika alkawurran zaben da suka yi.

Ya ce “Idan za a yi imani da kafafen sadarwa na zamani, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari yana rokon magajinsa, Bola Ahmed Tinubu da kada ya binciki wasu tsoffin jami’an gwamnatinsa.

“Karya ne, ba a tattauna wani abu makamacin haka ba. Wannan labarin karya ne, kuma ba wani abu ba. Alhamdulillahi ba kowa a dakin da suka hadu sai shugabannin biyu, don haka babu wanda ya isa ya kawo labarin tattaunawar tasu.

Duk mai yiwuwa, tsohon shugaban kasar yana fatan ya kasance a waje da abin da ya faru don kada ya dauke hankalin sabuwar gwamnati.

“Ya zabi ya koma gida Daura da fatan ya samu hutu ya kuma bai wa gwamnatin damar yin aikinta.

Ya ci gaba da cewa, “Ba abin da yake fatan samu face hutu, kuma gwamnatin Tinubu ta samu yanayi mai kyau na yin aiki kan cika alkawuran da suka dauka.”

Buhari
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Next Post
Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.