ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Musanta Hana Tinubu Binciken Tsofaffin Jami’an Gwamnatinsa 

by Abubakar Abba
3 years ago
Buhari

Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi kakkausar suka dangane da wani ikirari da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke nuna cewa ya bukaci magajinsa, Bola Ahmed Tinubu da ya daina binciken wasu tsoffin jami’an gwamnatinsa.

Da yake bayyana rahotannin a matsayin “labaran karya,” mai magana da yawun Buhari, Garba Shehu, a wata sanarwa da ya fitar, ya bukaci jama’a da kada su amince da irin wadannan bayanai marasa tushe.

  • Mataimakin Shugaban Kungiyar Miyetti Allah Ya Bace
  • NLC Za Ta Yi Zama Kan Hana Wasu Ma’aikatan Kano Albashi

A cewar Shehu, da gan-gan Buhari ya zabi ya ci mutuncinsa da kuma kaucewa jawo hankalinsa domin kaucewa duk wani abu da zai kawo wa sabuwar gwamnati cikas.

ADVERTISEMENT

Da yake neman zaman kadaici, ya ce tun da farko tsohon shugaban ya koma mahaifarsa ta Daura amma ya ga an gagara samun kwanciyar hankali da ake bukata saboda yawan masu ziyara.

Sakamakon haka, Shehu ya ce tsohon shugaban ya koma wani wurin da aka kebe, inda yake fatan samun hutun da ya ke nema.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

Shehu ya nanata muhimmancin yin watsi da wadannan ikirari marasa tushe, inda ya jaddada bukatar mayar da hankali kan bayanai na gaskiya da tabbatar da gaskiya.

A cewarsa, babban abin da tsohon shugaban kasar ya sa a gaba shi ne zaman lafiyarsa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu za ta yi aiki yadda ya kamata wajen cika alkawurran zaben da suka yi.

Ya ce “Idan za a yi imani da kafafen sadarwa na zamani, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari yana rokon magajinsa, Bola Ahmed Tinubu da kada ya binciki wasu tsoffin jami’an gwamnatinsa.

“Karya ne, ba a tattauna wani abu makamacin haka ba. Wannan labarin karya ne, kuma ba wani abu ba. Alhamdulillahi ba kowa a dakin da suka hadu sai shugabannin biyu, don haka babu wanda ya isa ya kawo labarin tattaunawar tasu.

Duk mai yiwuwa, tsohon shugaban kasar yana fatan ya kasance a waje da abin da ya faru don kada ya dauke hankalin sabuwar gwamnati.

“Ya zabi ya koma gida Daura da fatan ya samu hutu ya kuma bai wa gwamnatin damar yin aikinta.

Ya ci gaba da cewa, “Ba abin da yake fatan samu face hutu, kuma gwamnatin Tinubu ta samu yanayi mai kyau na yin aiki kan cika alkawuran da suka dauka.”

Buhari
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

June 12, 2026
Buhari
Manyan Labarai

June 12, 2026
Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya
Manyan Labarai

Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya

June 12, 2026
Next Post
Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.