• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku

by Isah Abdullahi
2 years ago
shagalinku

Fitaccen dan kasuwan nan da ke Zariya a Jihar Kaduna, Alhaji Umaru Shagalinku ya kai ziyarar ban girma ga Shugaban kasa, Muhammadu Buhar a fadar gwamna-tin tarayya da ke Abuja.

A lokacin wannan ziyarar, Alhaji Shagalinku ya bayyana cewa Shugaba Buhari ya yi iya bakin kokarinsa wajen kawar da matsalolin da suka addabi Nijeriya.

  • Buhari Ya Bukaci Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Mambobin Majalisar NEDC 12

Ya yaba wa Shugaban Buhari na yadda a shekara takwas da suka gabata ya yi duk abin da ya dace domin kawo karshen matsalolin da suke addabar Nijeriya da ku-ma ‘yan Nijeriya baki daya.

Alhaji Shagalinku ya ci gaba da cewa duk wanda ya san halin da Nijeriya ke ciki kafin zaben 2015, ya san Shugaban Buhari ya dauki matakai da dama domin kawo karshen matsalolin tsaro da ke neman durkusar da Nijeriya da kuma ‘yan Nijeriya, amma matakan da Shugaba Buhari ya dauka ya kawo mafita masu yawan gaske ga ‘yan Nijeriya, musamman a jihohin arewa da matsalolin tsaron suka fi yin ka-mari a baya.

A cewar Shagalinku, wadannan matakai da ya fara samun mafita ga matsalolin tsaro yana fatan zai ci gaba da nuna wa zababben shugaban kasa, Alhaji Ahmed Bola Tunubu hanyoyin da ya tsaya a kansu, domin samun mafita na karshe ga matsalolin tsaron Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

A game da bangaren noma kuma, Shagalinku ya ce an sami shekaru masu yawa da gwamnatocin da suka gabata ba su fito da tsare -tsaren da Shugaba Buhari ya fito da su ba, wanda duk wanda ke Nijeriya ya san an sami ci gaba a harkar noma, musamman a bangaren noman shinkafa da suka haifar da da mai ido ga manoman shinkafa a Nijeriya.

Ya shawarci sabon shugaban kasa mai jirar gado da ya dora daga wajen da Shugaban Buhari ya tsaya, domin al’ummar Nijeriya su dogara da shinkafar da ake nomawa a cikin gida.

Da yake mayar da jawabi, Shugaban Buhari ya fara da nuna jin dadinsa da wan-nan ziyara da Alhaji Umaru Shagalinku ya kai ma sa a fadar gwamnatin tarayya a Abuja.

Shugaba Buhari ya kuma yaba wa Alhaji Ummaru Shagalinku na yadda ya kwashe shekaru a harkar kasuwanci a sassan Nijeriya wanda ya samar wa dubban ‘yan Nijeriya sana’o’in dogaro da kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post
Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.