• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku

byIsah Abdullahi
2 years ago
shagalinku

Fitaccen dan kasuwan nan da ke Zariya a Jihar Kaduna, Alhaji Umaru Shagalinku ya kai ziyarar ban girma ga Shugaban kasa, Muhammadu Buhar a fadar gwamna-tin tarayya da ke Abuja.

A lokacin wannan ziyarar, Alhaji Shagalinku ya bayyana cewa Shugaba Buhari ya yi iya bakin kokarinsa wajen kawar da matsalolin da suka addabi Nijeriya.

  • Buhari Ya Bukaci Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Mambobin Majalisar NEDC 12

Ya yaba wa Shugaban Buhari na yadda a shekara takwas da suka gabata ya yi duk abin da ya dace domin kawo karshen matsalolin da suke addabar Nijeriya da ku-ma ‘yan Nijeriya baki daya.

Alhaji Shagalinku ya ci gaba da cewa duk wanda ya san halin da Nijeriya ke ciki kafin zaben 2015, ya san Shugaban Buhari ya dauki matakai da dama domin kawo karshen matsalolin tsaro da ke neman durkusar da Nijeriya da kuma ‘yan Nijeriya, amma matakan da Shugaba Buhari ya dauka ya kawo mafita masu yawan gaske ga ‘yan Nijeriya, musamman a jihohin arewa da matsalolin tsaron suka fi yin ka-mari a baya.

A cewar Shagalinku, wadannan matakai da ya fara samun mafita ga matsalolin tsaro yana fatan zai ci gaba da nuna wa zababben shugaban kasa, Alhaji Ahmed Bola Tunubu hanyoyin da ya tsaya a kansu, domin samun mafita na karshe ga matsalolin tsaron Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

A game da bangaren noma kuma, Shagalinku ya ce an sami shekaru masu yawa da gwamnatocin da suka gabata ba su fito da tsare -tsaren da Shugaba Buhari ya fito da su ba, wanda duk wanda ke Nijeriya ya san an sami ci gaba a harkar noma, musamman a bangaren noman shinkafa da suka haifar da da mai ido ga manoman shinkafa a Nijeriya.

Ya shawarci sabon shugaban kasa mai jirar gado da ya dora daga wajen da Shugaban Buhari ya tsaya, domin al’ummar Nijeriya su dogara da shinkafar da ake nomawa a cikin gida.

Da yake mayar da jawabi, Shugaban Buhari ya fara da nuna jin dadinsa da wan-nan ziyara da Alhaji Umaru Shagalinku ya kai ma sa a fadar gwamnatin tarayya a Abuja.

Shugaba Buhari ya kuma yaba wa Alhaji Ummaru Shagalinku na yadda ya kwashe shekaru a harkar kasuwanci a sassan Nijeriya wanda ya samar wa dubban ‘yan Nijeriya sana’o’in dogaro da kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post
Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version