Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

An Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Sassauta Farashin Kayayyaki

by Tayo Adelaja
September 15, 2017
in RAHOTANNI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abdullahi, Lafia

An bukaci ‘yan kasuwa a Jihar Nasarawa da su sassauta farashin kayayyakinsu ga mabukata domin kawo saukin matsanancin hali da al’umma ke ciki. Shugaban ‘yan kasuwar jihar, Alhaji Shammasu Dantsoho ne ya mika wannan bukatar jim kadan bayan kammala bikin rantsar da shi a matsayin shugaban kungiyar karo na biyu da sauran sabbin jami’an kungiyar a Lafia babban jihar.

Ya ce, mambobin kungiyar suna da rawar da za su taka wajen tabbattar da daidaito ga tattalin arzikin kasar nan ta hanyar daina boye da guje wa tsawwala farashin kayyayyaki. Ya ci gaba da cewa, kamata ya yi ‘yan kasuwa su rika kasancewa masu gaskiya da adalci cikin harkokinsu ta hanyar yin la’akari da halin da ‘yan Nijeriya ke ciki domin rage musu radadin yanayin.

Da yake yaba wa mambobin kungiyar kan goyon baya da suka ba shi na sake zabar sa a matsayin shugaban kungiyarsu, Dantsoho ya ce zai bai wa marada kunya dangane da amanar da suka damka masa. Yana mai cewa, zai kasance mai himma wajen sauke duk nauyin da aka dora masa.

Da yake jawabi a wajen bikin rantsarwar mai martaba Sarkin Lafia wanda ya samu wakilcin Tafarkin Lafia Alhaji Aliyu Ibrahim, ya shawarci sabbin shugabanin ‘yan kasuwar jihar da su kasance masu sadaukar da kai wajen tafiyar da harkokin kungiyar domin samar da cigaba. Sauran sabbin shugabannin da suka saba layar kama aiki sun hada da; Alhaji Baba Ali a matsayin mataimakin shugaba da Ibrahim Tanko a matsayin  sakatare da dai sauransu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Dillalai Da Makaranta Jarida Sun Jinjina Wa Fitowar LEADERSHIP A YAU

Next Post

Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Aikin Hanya A Kauru

RelatedPosts

Kayan Marmari

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Yi Gyara A Kan Tsarin Makarantun Islamiyya

by Sulaiman Ibrahim
12 hours ago
0

Daga Sagir Abubakar Katsina Majalissar zartarwa ta Jihar Katsina ta...

Korar Ma’aikata A Kaduna Ta Kara Jefa Jama’a Mawuyacin Hali – Isah Ashiru

Korar Ma’aikata A Kaduna Ta Kara Jefa Jama’a Mawuyacin Hali – Isah Ashiru

by Sulaiman Ibrahim
13 hours ago
0

Daga Abubakar Abba, Kaduna Dan takarar Gwamnan Jihar Kaduna karkashin...

Babandede Ya Yi Gargadi A Kan Daukan Aiki Na Bogi Da Sunan NIS

Sauye-sauye Masu Ma’ana A Sashen Fasfo Na Hukumar Shige Da Ficen Nijeriya

by Yahuzajere
2 days ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), karkashin...

Next Post

Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Aikin Hanya A Kauru

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version