• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

by Leadership Hausa
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoman Nijeriya kamar takwarorinsu na wasu kasashen Afrika suna fama da matsalar karancin Takin zamani, wanda shi ne daya daga cikin abubuwa masu muhimmanci da ake bukata a gona don samar da abinci tare da kawo karshen matsalar rashin abinci da ake fuskanta a kasar nan dama nahiyar Afrika gaba daya.

Dumamar yanayi da matsalolin da ya haifar ya kai ga tilasta amfani da Takin zamani a gonakinmu don kara bunkasa albarkar kasa wanda hakan zai kai ga samar da yabanya mai yawa.

  • Sin Ta Yi Watsi Da Rahoton MDD Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama A Xinjiang
  • Jami’an KAROTA Sun Cafke Tirela Makare Da Giya A Kano

Tabbas amfani da Takin zaman ya taimaka wajen samun karin girbin abin da aka shuka wanda hakan kuma yana taimakawa wajen tabbatar da wadatar abinci a fadin kasar nan dama yankin Afriki gaba daya.

Amma kuma duk da muhimmanci Takin zamani ga harkar noma a wannan lokacin, Takin ya yi matukar karanci ga shi kuma da tsananin tsada, Taki na neman gagarar kanana da matsakaitar manona, musamman ganin yadda aka siyasantar da rabawa in gwamnati ta samar don manona su amfana.

Bayani ya nuna cewa, a halin yanzu farashin Takin NPK da Urea ya kai Naira 20, 000 a kasuwannin mu.

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Abin takaici a nan shi ne yadda tallafin da gwamnati ke ikirarin tana sanya wa don amfanar talaka baya isa ga wadanda suka fi bukata, Takin ya fada hannun mugayen ‘yan kasuwa wadanda suka tsawalla masa kudi, suka kuma boye shi don a wasu wuraren ko da kudin ka samun Takin yana da mautukar wahala ga kanana da matsaikaitan manoma.

Mun damu matuka a kan karancin Takin zamani don kuwa hakan ya kara matsalar da manoman mu ke ciki ne, musamman ganin suna fuskantar matsaloli a wasu wuraren da suka hada da ayyukan ‘yanta’adda, wadannan matsaloli ne masu tayar da hankula don a wasu wuraren harkar noman ma ta tsaya cik.

Saboda haka fuskantar tsadar Takin zamani a irin wannan lokacin abu ne da zai dagula lissafin manoma gaba daya zai kuma haifar da karancin abinci a cikin al’umma.

Kwanakin baya, babban sakataren Kungiyar Masu Sarrafa Takin Zamani a Nijeriya, (FEPSAN), Gideon Nagedu ya yi ikirarin cewa, Takin Urea, ne kadai ake fuskantar karancinsa a Nijeriya, wai kuma hakan na faruwa ne saboda karancin Iskar Gas da ake fuskanta a Nijeriya, sai dai kuma wasu bayanai sun nuna cewa karancin Takin da ake fuskanta ba wai ya tsaya a kan Takin Urea kada ba ne.

 Duk kuwa cewa, muna sane da cewa, annobar cutar Korona da aka fuskanta a Duniya da yadda aka takaita zirga-zirga da kuma yakin da ake yi a halin yanzu a tsakanin Rasha da Yukiren ya taimaka wajen haifar da karancin Takin zamani, amma muna kira ga Gwamnati a dukkan matakai da su tabbatar da daukar matakan da suka dace don kawo kaeshen karancin Takin da ake fuskanta a halin yanzu don kuwa barazana ce ga samar da wadataccen abinci ga al’umma.

A daida wannan lokaci kuma ya kamata mu ne jin dalilin da ya sa Kamfanonin Takin Zamani na cikin gida suka kasa fuskantar samar da issasun takin zamanin ga manoman Nijeriya.

In har da gaske ake yi na kokarin samar da issashe Takin zamani ga manoman Nijeriya to ya zama tilas kamfanonin takin zmani na cikin gida su farfado don ganin sun cike gibin Takin da ke bukata a cikin gida har a fara tallafa wa wasu kasashen Afrika.

Wadannan matakan sun zama dole saboda ganin muhimmancin Takin zamani ga harkar noma a wannan lokacin.

Idan za a iya tunawa a shekarar 2016, gwamnatin tarayya ta sanya hannun a wata yarjejeniyar samar da Takin zamani tsakaninta da wani kamfanin kasar Morocco, an shirya amfani da Iskar Gas ta Nijeriya da kuma sinadarin phosphate daga kasar Maroco don samar da issashen Takin.

Gwamnati ta bayyana cewa, yarjejeniyar ta samar da shirin yadda za a yi amfani da Iskar Gas na Nijeriya da Phosphate daga kasar Moroco don samar da Tan 750,000 na sinadarin Ammonia da tan Miliyan daya na Takin Phosphate a duk shekara daga nan zuwa shekarar 2025.

Babu tantama zuba jari a bangaren samar da Takin zamani zai matukar taimakawa Nijeriya a kokarinta na samar da isashen abinci ga al’ummarta hakan kuma zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.

Dole a wannan gabar a yaba wa Kamfanin Dangote a bisa kokarinshi na samar da takin zamani a cikin gida ta yadda ya kafa katafaren kamfanin Takin zamani da aka kiyasta kudinsa ya kai Dala Biliyan 2.5.

Mun tabbatar da cewa, kamar mafi yawa ‘yan Nijeriya, Kamfanin Taki na Dangote zai bayar da gaggarumar gudummawa wajen ganin an samu wadataccen Takin zamani a kasa yayin da za a iya fitar da rarrar zuwa kasashe Afrika da sauran kasashen duniya.

Akwai dalilai da dama da dole gwamnati ta sanya hankali a kula da bangaren harkar noma, ciki kuwa akwai cewa a halin yanzu bangaren yana samar da aikin yi ga fiye da kashi 33 na ‘yan Nijeriya, gona ne kuma bangaren tattalin arzikin kasa da ya fi kowanne samar wa da al’umma aikin yi, don haka dole gwamnati ta sanya ido a kan ganin bunkasar bangaren.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dumamar YanayiGonakiManomaNijeriyaNomaRuwan SamaSaukiTaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

…Dalla-dallar Yadda Aka Kashe Kudin Tallafin Mai

Next Post

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

6 hours ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.