• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buni Ya Bukaci Kirista Su Yi Addu’ar Samun Nasarar Mika Mulki Ga Sabuwar Gwamnati

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Labarai
0
Buni Ya Bukaci Kirista Su Yi Addu’ar Samun Nasarar Mika Mulki Ga Sabuwar Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya bukaci mabiya addinin Kirista a Nijeriya su yi amfani da bikin Easter wajen yin addu’o’i na musamman domin samun nasarar mika mulki ga sabuwar gwamnati mai zuwa.

A sanarwar manema labaru mai sa-hannun mai magana da yawun gwamnan, Alhaji Mamman Mohammed ya ce, Buni ya sanar da hakan ne a sakonsa na bikin ranar Easter da ya aike wa mabiya addinin Kirista.

  • Da Dumi-dumi: APC Ta Dakatar Da Dan Majalisar Wakilai Shehu Koko 
  • Duk Da Tsadar Kujerar Aikin Hajjin Bana, Jihar Kaduna Na Bukatar Karin Kujera 500

Ya kara da cewa, abu ne mai mahimmanci a yi amfani da wannan lokacin wajen nuna kauna da soyayya tare da sadaukar wa a matsayin sakon da yake kunshe a bikin ranar Easter ga kasarmu Nijeriya.

“Kyakkyawan darasin da yake tattare da wannan rana shi ne kaunar juna da sadaukar wa, wanda suka dace a aiwatar da su wajen bunkasa zaman lafiya da hadin kai don ci gaban Nijeriya da ‘yan kasa baki daya.”

Har wala yau, gwamna Buni ya shaidar da cewa, wannan lokaci ne mai albarka wanda mabiya addinin Kirista suke gudanar da harkokin ibada a cikin na Easter, kuma a daidai lokacin da al’ammar musulmi suke gudanar da azumin watan Ramadan.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

“Wanda saboda haka, wannan babbar dama ce garemu a matsayin yan kasa, muyi amfani da wannan lokacin mu yi addu’o’i na musamman ga kasarmu.” In ji gwamna Buni.

Gwamnan ya jaddada kira ga shugabanin addini da na al’amma, kowane lokaci su rinka yin wa’azuka da kira wajen samun dawamamen zaman lafiya da fahimtar juna.

“Matikar mun aiwatar da koyarwar addininmu, zamu samu ci gaba mai dorewa ta hanyar samun zaman lafiya.”

“Saboda a ‘yan shekaru kadan da suka gabata, ba za mu iya zuwa masallatanmu da coci cikin nutsuwa ba a jihar Yobe, sakamakon matsalolin tsaro da muka sha fama dasu, amma yanzu cikin taimakon Allah, zaman lafiya ya dawo kowa yana harkokin sa cikin limana.”

“Bisa ga wannan, mu yaki son zuciya tare da yaki da shaidan don kaucewa abubuwan da za su harzuka mu aikata abin da zai kawo tashin-tashina a jiharmu ta Yobe da Nijeriya baki daya.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Mai Mala BuniYobeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Furucin Dakta Idris Kan Manzon Allah Ya Janyo Zafafan Muhawara A Bauchi

Next Post

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

Related

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

11 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

11 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

13 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

16 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

16 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

17 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

'Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.