• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buni Ya Bukaci Kirista Su Yi Addu’ar Samun Nasarar Mika Mulki Ga Sabuwar Gwamnati

by Muhammad Maitela
2 years ago
Buni

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya bukaci mabiya addinin Kirista a Nijeriya su yi amfani da bikin Easter wajen yin addu’o’i na musamman domin samun nasarar mika mulki ga sabuwar gwamnati mai zuwa.

A sanarwar manema labaru mai sa-hannun mai magana da yawun gwamnan, Alhaji Mamman Mohammed ya ce, Buni ya sanar da hakan ne a sakonsa na bikin ranar Easter da ya aike wa mabiya addinin Kirista.

  • Da Dumi-dumi: APC Ta Dakatar Da Dan Majalisar Wakilai Shehu Koko 
  • Duk Da Tsadar Kujerar Aikin Hajjin Bana, Jihar Kaduna Na Bukatar Karin Kujera 500

Ya kara da cewa, abu ne mai mahimmanci a yi amfani da wannan lokacin wajen nuna kauna da soyayya tare da sadaukar wa a matsayin sakon da yake kunshe a bikin ranar Easter ga kasarmu Nijeriya.

“Kyakkyawan darasin da yake tattare da wannan rana shi ne kaunar juna da sadaukar wa, wanda suka dace a aiwatar da su wajen bunkasa zaman lafiya da hadin kai don ci gaban Nijeriya da ‘yan kasa baki daya.”

Har wala yau, gwamna Buni ya shaidar da cewa, wannan lokaci ne mai albarka wanda mabiya addinin Kirista suke gudanar da harkokin ibada a cikin na Easter, kuma a daidai lokacin da al’ammar musulmi suke gudanar da azumin watan Ramadan.

LABARAI MASU NASABA

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

“Wanda saboda haka, wannan babbar dama ce garemu a matsayin yan kasa, muyi amfani da wannan lokacin mu yi addu’o’i na musamman ga kasarmu.” In ji gwamna Buni.

Gwamnan ya jaddada kira ga shugabanin addini da na al’amma, kowane lokaci su rinka yin wa’azuka da kira wajen samun dawamamen zaman lafiya da fahimtar juna.

“Matikar mun aiwatar da koyarwar addininmu, zamu samu ci gaba mai dorewa ta hanyar samun zaman lafiya.”

“Saboda a ‘yan shekaru kadan da suka gabata, ba za mu iya zuwa masallatanmu da coci cikin nutsuwa ba a jihar Yobe, sakamakon matsalolin tsaro da muka sha fama dasu, amma yanzu cikin taimakon Allah, zaman lafiya ya dawo kowa yana harkokin sa cikin limana.”

“Bisa ga wannan, mu yaki son zuciya tare da yaki da shaidan don kaucewa abubuwan da za su harzuka mu aikata abin da zai kawo tashin-tashina a jiharmu ta Yobe da Nijeriya baki daya.” In ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati
Labarai

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

'Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.