• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buni Ya Bukaci Kirista Su Yi Addu’ar Samun Nasarar Mika Mulki Ga Sabuwar Gwamnati

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Labarai
0
Buni Ya Bukaci Kirista Su Yi Addu’ar Samun Nasarar Mika Mulki Ga Sabuwar Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya bukaci mabiya addinin Kirista a Nijeriya su yi amfani da bikin Easter wajen yin addu’o’i na musamman domin samun nasarar mika mulki ga sabuwar gwamnati mai zuwa.

A sanarwar manema labaru mai sa-hannun mai magana da yawun gwamnan, Alhaji Mamman Mohammed ya ce, Buni ya sanar da hakan ne a sakonsa na bikin ranar Easter da ya aike wa mabiya addinin Kirista.

  • Da Dumi-dumi: APC Ta Dakatar Da Dan Majalisar Wakilai Shehu Koko 
  • Duk Da Tsadar Kujerar Aikin Hajjin Bana, Jihar Kaduna Na Bukatar Karin Kujera 500

Ya kara da cewa, abu ne mai mahimmanci a yi amfani da wannan lokacin wajen nuna kauna da soyayya tare da sadaukar wa a matsayin sakon da yake kunshe a bikin ranar Easter ga kasarmu Nijeriya.

“Kyakkyawan darasin da yake tattare da wannan rana shi ne kaunar juna da sadaukar wa, wanda suka dace a aiwatar da su wajen bunkasa zaman lafiya da hadin kai don ci gaban Nijeriya da ‘yan kasa baki daya.”

Har wala yau, gwamna Buni ya shaidar da cewa, wannan lokaci ne mai albarka wanda mabiya addinin Kirista suke gudanar da harkokin ibada a cikin na Easter, kuma a daidai lokacin da al’ammar musulmi suke gudanar da azumin watan Ramadan.

Labarai Masu Nasaba

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

“Wanda saboda haka, wannan babbar dama ce garemu a matsayin yan kasa, muyi amfani da wannan lokacin mu yi addu’o’i na musamman ga kasarmu.” In ji gwamna Buni.

Gwamnan ya jaddada kira ga shugabanin addini da na al’amma, kowane lokaci su rinka yin wa’azuka da kira wajen samun dawamamen zaman lafiya da fahimtar juna.

“Matikar mun aiwatar da koyarwar addininmu, zamu samu ci gaba mai dorewa ta hanyar samun zaman lafiya.”

“Saboda a ‘yan shekaru kadan da suka gabata, ba za mu iya zuwa masallatanmu da coci cikin nutsuwa ba a jihar Yobe, sakamakon matsalolin tsaro da muka sha fama dasu, amma yanzu cikin taimakon Allah, zaman lafiya ya dawo kowa yana harkokin sa cikin limana.”

“Bisa ga wannan, mu yaki son zuciya tare da yaki da shaidan don kaucewa abubuwan da za su harzuka mu aikata abin da zai kawo tashin-tashina a jiharmu ta Yobe da Nijeriya baki daya.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Mai Mala BuniYobeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Furucin Dakta Idris Kan Manzon Allah Ya Janyo Zafafan Muhawara A Bauchi

Next Post

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

Related

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara
Tsaro

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

9 minutes ago
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru
Labarai

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

13 minutes ago
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

24 minutes ago
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe
Labarai

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

3 hours ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

5 hours ago
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

14 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

'Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.