ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buni Ya Bukaci Kirista Su Yi Addu’ar Samun Nasarar Mika Mulki Ga Sabuwar Gwamnati

by Muhammad Maitela
3 years ago
Buni

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya bukaci mabiya addinin Kirista a Nijeriya su yi amfani da bikin Easter wajen yin addu’o’i na musamman domin samun nasarar mika mulki ga sabuwar gwamnati mai zuwa.

A sanarwar manema labaru mai sa-hannun mai magana da yawun gwamnan, Alhaji Mamman Mohammed ya ce, Buni ya sanar da hakan ne a sakonsa na bikin ranar Easter da ya aike wa mabiya addinin Kirista.

  • Da Dumi-dumi: APC Ta Dakatar Da Dan Majalisar Wakilai Shehu Koko 
  • Duk Da Tsadar Kujerar Aikin Hajjin Bana, Jihar Kaduna Na Bukatar Karin Kujera 500

Ya kara da cewa, abu ne mai mahimmanci a yi amfani da wannan lokacin wajen nuna kauna da soyayya tare da sadaukar wa a matsayin sakon da yake kunshe a bikin ranar Easter ga kasarmu Nijeriya.

ADVERTISEMENT

“Kyakkyawan darasin da yake tattare da wannan rana shi ne kaunar juna da sadaukar wa, wanda suka dace a aiwatar da su wajen bunkasa zaman lafiya da hadin kai don ci gaban Nijeriya da ‘yan kasa baki daya.”

Har wala yau, gwamna Buni ya shaidar da cewa, wannan lokaci ne mai albarka wanda mabiya addinin Kirista suke gudanar da harkokin ibada a cikin na Easter, kuma a daidai lokacin da al’ammar musulmi suke gudanar da azumin watan Ramadan.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Wanda saboda haka, wannan babbar dama ce garemu a matsayin yan kasa, muyi amfani da wannan lokacin mu yi addu’o’i na musamman ga kasarmu.” In ji gwamna Buni.

Gwamnan ya jaddada kira ga shugabanin addini da na al’amma, kowane lokaci su rinka yin wa’azuka da kira wajen samun dawamamen zaman lafiya da fahimtar juna.

“Matikar mun aiwatar da koyarwar addininmu, zamu samu ci gaba mai dorewa ta hanyar samun zaman lafiya.”

“Saboda a ‘yan shekaru kadan da suka gabata, ba za mu iya zuwa masallatanmu da coci cikin nutsuwa ba a jihar Yobe, sakamakon matsalolin tsaro da muka sha fama dasu, amma yanzu cikin taimakon Allah, zaman lafiya ya dawo kowa yana harkokin sa cikin limana.”

“Bisa ga wannan, mu yaki son zuciya tare da yaki da shaidan don kaucewa abubuwan da za su harzuka mu aikata abin da zai kawo tashin-tashina a jiharmu ta Yobe da Nijeriya baki daya.” In ji shi.

Buni
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

'Yansanda Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.