ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burin Kasar Sin Shi Ne “A Gudu Tare A Tsira Tare”

by CMG Hausa
4 years ago
G20

Yayin da ake ci gaba da gudanar da taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobin kungiyar G20, a tsibirin Bali na kasar Indonesia, hankula na karkata ga ganawar da manyan jami’an sassan kasashe daban daban, mahalarta taron za su gudanar.

Cikin irin wadannan ganawa, akwai wadda aka tsara gudanar ta tsakanin ministan wajen kasar Sin Wang Yi, da sakataren wajen Amurka Antony Blinken, a gefen taron mai matukar muhimmanci.

  • Kasar Sin Ta Jaddada Matsayinta Game Da Batutuwan Da Suka Shafi Yankin Taiwan Da Xinjiang

Masharhanta dai na ganin idan har ana son cimma gajiya daga ganawar sassan biyu, to ya zama wajibi bangaren Amurka ya nuna sahihanci, da yin magana daya, ta yadda hakan zai haifar da amincewar juna, da kyautata alakar kasashen 2 yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa an kafa kungiyar G20 ne da nufin warware manyan matsalolin tattalin arzikin duniya, kamar daidaita yanayin hada hadar kudade, da dakile sauyin yanayi, da wanzar da ci gaban duniya mai dorewa.

A bangaren Sin da Amurka, akwai karin batutuwa da ya wajaba sassan 2 su kara maida hankali a kan su, musamman ma batun sabanin su game da kare ikon mulkin kai, da tsaro, da harkokin kasuwanci, da kyautata diflomasiyya.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Har kullum, manufar kasar Sin ba ta sauyawa, game da burinta na ganin sassan duniya sun yi tafiya tare, domin cimma moriyar juna, da samar da al’ummar duniya mai makomar bai daya ga dukkanin bil adama.

A wannan gaba, fatan da yawa daga masu fashin baki, shi ne yayin ganawar kai tsaye ta wadannan manyan jami’ai biyu, bangaren Amurka zai amince da muradun kasar Sin, na kauracewa tsoma baki cikin harkokinta na cikin gida, musamman ma batun yankin Taiwan, wanda a baya bayan nan Amurkan ke ta aiwatar da wasu matakai, wadanda ba za su haifar da da mai ido ba.

Cikin irin wadanan matakai akwai batun karfafa ayyukan sojinta, da na tattalin arziki, da kawance da kasashen gabashin Asiya, a wani yunkuri na abun da take kira “Dakile fadadar tasirin kasar Sin”.

Don haka dai ana iya cewa, dangantaka tsakanin Amurka da Sin a wannan lokaci, na cikin wani yanayi mai sarkakiya. Duk da cewa jami’an sassan biyu na ganawa, da tattaunawa sa’i sa’i. Burin kowa a yanzu, bai wuce ganin manyan kasashen 2 sun fahimci juna ba.

Kana su kauracewa dukkanin wani nau’i na fito na fito, tare da rungumar matakan da za su amfani al’ummun su da duniya baki daya. (Saminu Hassan)

G20
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola

NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.