• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burin Kasar Sin Shi Ne “A Gudu Tare A Tsira Tare”

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Burin Kasar Sin Shi Ne “A Gudu Tare A Tsira Tare”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ake ci gaba da gudanar da taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobin kungiyar G20, a tsibirin Bali na kasar Indonesia, hankula na karkata ga ganawar da manyan jami’an sassan kasashe daban daban, mahalarta taron za su gudanar.

Cikin irin wadannan ganawa, akwai wadda aka tsara gudanar ta tsakanin ministan wajen kasar Sin Wang Yi, da sakataren wajen Amurka Antony Blinken, a gefen taron mai matukar muhimmanci.

  • Kasar Sin Ta Jaddada Matsayinta Game Da Batutuwan Da Suka Shafi Yankin Taiwan Da Xinjiang

Masharhanta dai na ganin idan har ana son cimma gajiya daga ganawar sassan biyu, to ya zama wajibi bangaren Amurka ya nuna sahihanci, da yin magana daya, ta yadda hakan zai haifar da amincewar juna, da kyautata alakar kasashen 2 yadda ya kamata.

Duk da cewa an kafa kungiyar G20 ne da nufin warware manyan matsalolin tattalin arzikin duniya, kamar daidaita yanayin hada hadar kudade, da dakile sauyin yanayi, da wanzar da ci gaban duniya mai dorewa.

A bangaren Sin da Amurka, akwai karin batutuwa da ya wajaba sassan 2 su kara maida hankali a kan su, musamman ma batun sabanin su game da kare ikon mulkin kai, da tsaro, da harkokin kasuwanci, da kyautata diflomasiyya.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

Har kullum, manufar kasar Sin ba ta sauyawa, game da burinta na ganin sassan duniya sun yi tafiya tare, domin cimma moriyar juna, da samar da al’ummar duniya mai makomar bai daya ga dukkanin bil adama.

A wannan gaba, fatan da yawa daga masu fashin baki, shi ne yayin ganawar kai tsaye ta wadannan manyan jami’ai biyu, bangaren Amurka zai amince da muradun kasar Sin, na kauracewa tsoma baki cikin harkokinta na cikin gida, musamman ma batun yankin Taiwan, wanda a baya bayan nan Amurkan ke ta aiwatar da wasu matakai, wadanda ba za su haifar da da mai ido ba.

Cikin irin wadanan matakai akwai batun karfafa ayyukan sojinta, da na tattalin arziki, da kawance da kasashen gabashin Asiya, a wani yunkuri na abun da take kira “Dakile fadadar tasirin kasar Sin”.

Don haka dai ana iya cewa, dangantaka tsakanin Amurka da Sin a wannan lokaci, na cikin wani yanayi mai sarkakiya. Duk da cewa jami’an sassan biyu na ganawa, da tattaunawa sa’i sa’i. Burin kowa a yanzu, bai wuce ganin manyan kasashen 2 sun fahimci juna ba.

Kana su kauracewa dukkanin wani nau’i na fito na fito, tare da rungumar matakan da za su amfani al’ummun su da duniya baki daya. (Saminu Hassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Sanda Sun Cafke Wasu Da Ake Zargi Da Laifin Fashi Da Makami A Wani Otal A Legas

Next Post

NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola

Related

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

6 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Daga Birnin Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

7 hours ago
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

8 hours ago
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

9 hours ago
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

10 hours ago
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

11 hours ago
Next Post
NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola

NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.