• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

by Leadership Hausa
4 days ago
in Siyasa
0
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yanzu haka dai cacar baki ta ɓarke tsakanin tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da jam’iyyar APC mai mulkin Nijeriya kan tallar tazarcen Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a 2027.

El-Rufai wanda ya kasance tsohon ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, ya yi gargaɗi cewa Nijeriya za ta iya rushewa kwata-kwata idan Shugaba Tinubu ya sami nasara a wa’adin mulki na biyu a 2027.

  • INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12
  • Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

El-Rufai ya bayar da wannan gargaɗin ne a Jihar Sakkwato a lokacin kamfen da haɗakar jam’iyyar adawa ta ADC ta shirya a ƙarshen mako.

Sai dai daraktan yaɗa labarai na APC, Bala Ibrahim, ya bayyana shugabannin ADC a matsayin tarin ‘yan siyasa da suke cikin ruɗani waɗanda ba su da abin da za su iya yi wa ‘yan Nijeriya.

Idan za a iya tunawa dai shugabannin adawa sun amince da ADC a matsayin jam’iyyar da za ta ƙalubalanci Shugaba Tinubu a zaɓen 2027.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

Mambobin haɗakar jam’iyar sun ƙunshi tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi da tsohon gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal da tsohon shugaban jam’iyyar APC, John Oyegun, da sauran manyan mutane da dama.

A cikin wannan tsarin, haɗakar jam’iyyar ta naɗa tsohon shugaban majalisar dattawa, Daɓid Mark da tsohon ministan cikin gida, Rauf Aregbesola, a matsayin shugaban da sakatare na riƙon ƙwarya.

Tun daga wannan lokaci, jam’iyyar tana ta karɓar masu sauya sheƙa daga sauran jam’iyyun adawa da kuma gudanar da tarurruka domin ƙara masun mambobi a faɗin ƙasar nan kafin zaɓen 2027.

El-Rufai, wanda ya kasance ɗaya daga cikin asalin mambobin APC, ya fice zuwa jam’iyyar SDP a rubi’in farko na wannan shekarar. Haka kuma ya kasance cikin jam’iyyar haɗaka ta ADC.

Ya bayyana cikakken goyon bayansa ga ADC kuma ya yi alƙawarin taimakawa wajen jan hankali ‘yan Nijeriya domin tabbatar da cewa APC ta sha kaye a 2027 a lokacin taron Sakkwato.

Tsohon gwamnan Kaduna ya jaddada cewa idan Tinubu ya samu wa’adi na biyu zai zama barazana mai tsanani ga makomar ƙasar nan.

“Na yi imanin cewa in muka yarda wannan jam’iyya da gwamnatinta ta ci gaba da mulki a zango na biyu, za ta wawuri dukkan abin da ya rage na tattalin arzikin Nijeriya, kuma ba za mu sami ɓarɓushin ƙasarmu ba ko kaɗan. Don haka, wannan yaƙi ne don rayukanmu,” in ji shi.

El-Rufai ya ce dawowarsa cikin harkokin siyasa ba ta ƙashin kansa ba, said ai akwai buƙatar dawowarsa don yaƙar gazawar wannan gwamnati.

Da yake mayar wa El-Rufai martani, sakataren jam’iyyar APC na ƙasa, Sanata Ajibola Basiru, ya buƙaci El-Rufai ya dakatar da yaƙin neman zaɓe 2027 har sai lokaci ya yi, kuma ya jira ya gani yadda jam’iyya mai mulki za ta ƙara yin nasara.

Sakataren APC ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai ta wayar tarho a ƙarshen mako.

Yayin da yake martanin, sakatare APC ya yi kira ga tsohon Gwamnan Jihar Kaduna da ya nemi aiki yi da zai sa ya zama mara zaman banza kafin zaɓen 2027.

Ya nuna cewa za a bayyana jadawalin zaɓen 2027 ne a watan Fabrairun 2026, ya yi mamakin yadda tsohon gwamnan Jihar Kaduna ya fara yaƙin neman zaɓen da ya rage saura shekara biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCEl-RufaiYelwatza
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Next Post

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Related

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

1 day ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

1 day ago
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
Siyasa

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

3 days ago
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10
Siyasa

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

4 days ago
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
Siyasa

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

5 days ago
Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman
Siyasa

Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman

5 days ago
Next Post
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

August 13, 2025
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.