• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Canada Za Ta Caka Wa Kanta Wuka Kan Matakin Da Ta Dauka A Kan Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Canada

Kwanan baya, gwamnatin kasar Canada ta gabatar da sabunta rahoton kudinta mai taken “sanarwar tattalin arziki a lokacin kaka”, inda ta yi shirin kara dora haraji kan wasu kayayyaki masu aiki da makamashin hasken rana da wasu ma’adanai da za su shigo daga kasar Sin a farkon shekarar badi. Ban da wannan kuma, rahoton ya bayyana shirin ware kudi dala miliyan 903 cikin shekaru 6 masu zuwa a bangaren kare tsaron iyakokinta.

Manazarta na ganin cewa, Canada na shirin daukar matakin kare tsaron iyakokinta da kara dorawa kasar Sin haraji ne don nuna biyayyarta ga Amurka, duba da cewa zababben shugaban Amurka Donald Trump ya taba yin barazanar kara dorawa kayayyakin da za a shigo da su daga Canada haraji da kashi 25%, da zarar ya hau kujerarsa.

  • NDLEA Ta Kama Mutane 415, Ta Ƙwace Tan 1.2 Na Ƙwayoyi A Bauchi
  • Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Dokar Haraji – Tinubu

Kazalika, daga baya, ya kara kawowa Canada barazana bisa hujjar tsaron iyaka da rashin samun dacewa tsakanin matakan da bangarorin biyu suka dauka kan haraji da suke son aiwatarwa a kan kasar Sin. Don haka gwamantin Justin Trudeau na kwadayin Amurka ta soke barazanar da Trump ya yi ta karawa Canada haraji bisa wadannan matakan da ya dauka.

Amma, matakan da Trudeau ya dauka za su tafi a banza, saboda Donald Trump dan kasuwa ne, tunaninsa na neman samun moriya mafi girma ba zai canja ba, baya ga haka yana mai da moriyar gwamnatinsa a gaban komai, ba zai yi la’akari da muradun kawayen kasarsa ba ko kadan.

Nuna biyayya ga Amurka don neman samun moriyar siyasa a gajeren lokaci, ba shakka ba wai zai illata huldar ciniki tsakanin Sin da Canada ne kawai ba, abin zai shafi hatta ‘yancinta na gudanar da harkokin kasa da kasa wanda zai bace sannu a hankali, kuma daga bisani za ta zama ’yar amshin shatan Amurka kurum! (Mai zane da rubutu: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Next Post
Filato

An Kashe Mutane 14 A Wani Sabon Harin Filato

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Canada

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.