• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Canada Za Ta Caka Wa Kanta Wuka Kan Matakin Da Ta Dauka A Kan Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Canada Za Ta Caka Wa Kanta Wuka Kan Matakin Da Ta Dauka A Kan Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, gwamnatin kasar Canada ta gabatar da sabunta rahoton kudinta mai taken “sanarwar tattalin arziki a lokacin kaka”, inda ta yi shirin kara dora haraji kan wasu kayayyaki masu aiki da makamashin hasken rana da wasu ma’adanai da za su shigo daga kasar Sin a farkon shekarar badi. Ban da wannan kuma, rahoton ya bayyana shirin ware kudi dala miliyan 903 cikin shekaru 6 masu zuwa a bangaren kare tsaron iyakokinta.

Manazarta na ganin cewa, Canada na shirin daukar matakin kare tsaron iyakokinta da kara dorawa kasar Sin haraji ne don nuna biyayyarta ga Amurka, duba da cewa zababben shugaban Amurka Donald Trump ya taba yin barazanar kara dorawa kayayyakin da za a shigo da su daga Canada haraji da kashi 25%, da zarar ya hau kujerarsa.

  • NDLEA Ta Kama Mutane 415, Ta Ƙwace Tan 1.2 Na Ƙwayoyi A Bauchi
  • Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Dokar Haraji – Tinubu

Kazalika, daga baya, ya kara kawowa Canada barazana bisa hujjar tsaron iyaka da rashin samun dacewa tsakanin matakan da bangarorin biyu suka dauka kan haraji da suke son aiwatarwa a kan kasar Sin. Don haka gwamantin Justin Trudeau na kwadayin Amurka ta soke barazanar da Trump ya yi ta karawa Canada haraji bisa wadannan matakan da ya dauka.

Amma, matakan da Trudeau ya dauka za su tafi a banza, saboda Donald Trump dan kasuwa ne, tunaninsa na neman samun moriya mafi girma ba zai canja ba, baya ga haka yana mai da moriyar gwamnatinsa a gaban komai, ba zai yi la’akari da muradun kawayen kasarsa ba ko kadan.

Nuna biyayya ga Amurka don neman samun moriyar siyasa a gajeren lokaci, ba shakka ba wai zai illata huldar ciniki tsakanin Sin da Canada ne kawai ba, abin zai shafi hatta ‘yancinta na gudanar da harkokin kasa da kasa wanda zai bace sannu a hankali, kuma daga bisani za ta zama ’yar amshin shatan Amurka kurum! (Mai zane da rubutu: MINA)

Labarai Masu Nasaba

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NDLEA Ta Kama Mutane 415, Ta Ƙwace Tan 1.2 Na Ƙwayoyi A Bauchi

Next Post

An Kashe Mutane 14 A Wani Sabon Harin Filato

Related

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

5 days ago
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

6 days ago
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

1 week ago
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

1 week ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

2 weeks ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

2 weeks ago
Next Post
Filato

An Kashe Mutane 14 A Wani Sabon Harin Filato

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.