ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Taron Hadin Kan Maz’habobin Musulunci Ya Gudana A Saudiyya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Musulunci

Malaman addinin Musulunci sun gudanar da wani gagarumin taron hadin kai a tsakanin maz’habobi da darikun Musulunci a Makkah domin dinke baraka da rarrabuwar kai da ake samu a tsakaninsu.

Taron mai taken,“Gina gada tsakanin maz’habobin Musulunci da dariku”, ya samu halartar mabiya maz’habobi da darikun Musulunci daga ko ina a fadin duniya.

  • Hajjin Bana: Karin Naira Miliyan 1.9 Ya Jefa Dubban Maniyyata Cikin Garari
  • Mace Za Ta Iya Yin I’itikafi A Wannan Zamanin?

Kungiyar Kasashe Musulmi (MWL) ta shirya taron wanda Sarkin Saudiyya, Salman Bin Abdulaziz ya dauki nauyi. Malaman da suka halarci taron, sun bayyana aniyarsu ta inganta mu’amala domin farfado da gudunmawar da al’ummar Musulmi ke bayarwa wajen wayar da kan jama’a da samun ci gaba a duniya.

ADVERTISEMENT

Shugaban kungiyar ta MWL, Mohammed Al-Issa, ya bayyana wani shiri da taron ya amince da shi na samar da daftarin da za a yi aiki da shi wajen tabbatar hadin kai a tsakanin maz’habobi da darikun Musulunci don tunkarar dimbin kalubalen da suka addabi Musulmi a duniya.

Haka kuma Al-Issa ya bayyana farin cikinsa da karbar bakuncin taron mai dimbin tarihi a Makkah tare da jaddada bukatar hadin kan al’ummar Musulmi.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Sai dai ya yi gargadi game da kalaman bangaranci, ya kuma yi kira da a rika yada labaran da suka dace a kafafen yada labarai da ke kara samar da hadin kai. Ya mika godiyarsa ga mahukuntan kasar Saudiyya kan goyon bayan da suke ba su tare da yin addu’ar Allah ya kara ba su nasara.

A jawabinsa, Babban Mufti na Saudiyya, Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh, wanda Dakta Fahd Al-Majid ya gabatar, ya jaddada muhimmancin hadin kan al’ummar Musulmi, tare da tsawatarwa kan illar rarrabuwar kawuna kana ya bayyana irin gudunmawar da malamai ke bayarwa wajen samar da hadin kai a tsakanin Musulmai.

Ya gode wa Babban Hadimin Masallatai Masu Alfarma Guda Biyu, Sarki Salman Bin Abdulaziz kan goyon bayan taron tare da yaba wa kokarin hadin kan musulmai karkashin jagorancin Yarima Mohammed Bin Salman kuma Firayim Ministan Saudiyya.
Shi kuwa a nashi bangaren, Babban sakataren Kungiyar Hadin kan Musulmi (OIC), Hissein Brahim Taha ya yaba wa Sarki Salman da Yarima mai jiran gado Mohammed bisa goyon bayan shirya taron. Ya tabbatar da cewa muhimmin taron zai inganta hadin kai a tsakanin maz’habobi da darikun Musulunci tare da shawarwarin da za a yi amfani da su wajen samar da hadin kai da magance sabani.

Taha ya kuma yaba wa kungiyar MWL bisa sadaukarwar da take yi wa Musulunci da Musulman duniya baki daya.

A gefe guda kuma, an sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin kungiyoyin MWL da OIC kan hadin kai.

An rattaba hannu kan wata yarjejeniya tsakanin Cibiyar Fikhu ta Musulunci ta MWL da Cibiyar Nazarin Fikhu ta kasa da kasa ta OIC domin bunkasa hadin gwiwa a fannin bincike.

Wasu malamai na ganin wannan taron zai cimma nasara, yayin da wasu ke ganin har yanzu da sauran rina a kaba.

Babban limamin masallacin rukunin gidaje na Lake Biew Phase 2 da ke Abuja, Malam Falalu Abdullahi ya bayyana cewa, tun lokacin da hukumomin Saudiyya suka dage dokar hana wadanda ba Musulmai shiga Harami ba suka sauka daga layi. Ya ce irin wannan taro ba zai samu nasara ba har sai mahukunta kasar sun dawo kan layi.

Yayin da shi kuwa, Malam Bello Abukakar ke da ra’ayin cewa lallai wannan taron zai samu nasara. Ya ce kiran mabiya maz’habobi da darikun Musulmi wurin guda da aka yi shi kansa babban nasara ce.

Ya kara da cewa yana da yakinin wannan taro zai samu nasarar hada kan al’ummar Musulmin duniya matukar kowane dan maz’haba zai amince da hadin kan Musulunci fiye da daukaka maz’haba ko darikar ko kungiyarsa.

Musulunci
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Chelsea Za Ta Fafata Da Real Madrid Da Manchester City A Amurka

Chelsea Za Ta Fafata Da Real Madrid Da Manchester City A Amurka

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.