• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

China Ta Musanta Daukar Nauyin Ta’addanci A Nijeriya

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
China Ta Musanta Daukar Nauyin Ta’addanci A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin jakadancin China da ke Nijeriya ya musanta rahotannin da ke cewa yana daukar nauyin ayyukan ta’addanci a kasar a fakaice.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin ya wallafa a shafinsa na yanar gizo ya karyata rahoton da jaridar The Times of the UK ta wallafa, inda ta ce “Beijing na ba da tallafin ta’addanci a kaikaice” a Nijeriya.

  • Xi Ya Aika Sakon Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafa Jami’ar Yunnan
  • Da Dumi-Dumi: An Ga Watan Shawwal A Saudiyya

China ta ce rahoton ya samo asali ne daga bayanan da ba a tantance ba da kuma wadanda ba a tabbatar da su ba.

“Gwamnatin kasar Sin, da ofishin jakadancin kasar Sin da ke Nijeriya, a ko dabyaushe, suna karfafawa tare da yin kira ga kamfanoni da ‘yan kasar Sin da ke Nijeriya, da su kiyaye dokoki da ka’idojin Nijeriya, tare da aiwatar da dokokin gida da jagororin aiki, da muhalli, da lafiya da aminci, da sauransu, kuma za su ci gaba da kokarinsu a wannan fanni.

“Gwamnatin kasar Sin ta kasance kuma ba za ta taba shiga cikin kowane nau’i na taimakon ta’addanci ba.

Labarai Masu Nasaba

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

“Zarge-zargen da ke kunshe a cikin rahoton ba su da tushe balle makama, kuma rashin da’a ne, kuma an yi la’akari da manufar rahoton.

“A cikin shekaru da dama da suka gabata, hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen Sin da Nijeriya ya kawo fa’ida ta gaske ga alakar da ke tsakanin kasashen biyu da kyautata jin dadin jama’ar kasashen biyu.

“Za mu ci gaba da yin aiki tare da gwamnatin Nijeriya don inganta ci gaba da magance matsalolin tsaro, muna maraba da abokan huldar kasa da kasa da su shiga kokarinmu da gaskiya, amma za mu yi watsi da duk wani shiri ko matakin da zai bata mana hadin gwiwa,” in ji ofishin jakadancin a cikin sanarwar.

Rahoton a cikin The Times da aka buga a ranar 15 ga Afrilu, 2023 ya yi ikirarin cewa Beijing na ba da tallafin ta’addanci a kaikaice a Nijeriya don ruguza mafi girman tattalin arziki a Afirka.

A cewar rahoton, shugabannin ma’adinai na kasar Sin suna ba da tallafin kungiyoyin ‘yan ta’addan Nijeriya domin samun damar shiga ma’adinan kasar.

“Kamfanonin China da ke aiki a wasu sassan Nijeriya inda ake yawan kai hare-hare na kulla huldar tsaro da masu tada kayar baya…, in ji wani bangare na rahoton.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ChinaDaukar Nauyin Ta'addanciMusantawaNijeriyaRahoto
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: An Ga Watan Shawwal A Saudiyya

Next Post

Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

Related

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

1 hour ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

6 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

6 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

10 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

21 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

22 hours ago
Next Post
Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

June 27, 2025
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

June 27, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.