• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaba Da Musaya Zai Ingiza Kyautatuwar Aminci Tsakanin Sin Da Amurka

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaba Da Musaya Zai Ingiza Kyautatuwar Aminci Tsakanin Sin Da Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da manyan jami’an Sin da na Amurka ke kara bunkasa musaya tsakaninsu, masharhanta na kallon hakan a matsayin hanya mafi dacewa, ta farfado da alakarsu, tare da kawar da tarnakin dake mayar da hannun agogo baya, a wannan muhimmiyar dangantaka mai tasiri ga su kansu kasashen biyu, da ma sauran sassan duniya baki daya.

A baya bayan nan, mamban hukumar siyasa, kana direktan ofishin hukumar kula da harkokin waje ta kwamitin kolin JKS, Wang Yi ya gana da sakataren wajen Amurka Antony Blinken a birnin Jakarta, a gefen taron ministocin kasashe mambobin kungiyar ASEAN, inda suka yi musaya don gane da batutuwan dake jan hankalin kasashensu. Kaza lika kafin hakan mista Blinken ya ziyarci kasar Sin a watan Yuni da ya gabata, baya ga ziyarar da sakatariyar baitulmalin Amurka Janet Yellen ta kai kasar Sin, tare da zantawa da firaministan kasar Li Qiang, da ma mataimaki sa He Lifeng a farkon watan nan na Yuli. Har ila yau, wakilin musamman na shugaban kasar Amurka game da sauyin yanayi John Kerry, shi ma ya ziyarci kasar Sin ba da jimawa ba, inda ya tattaunawa da manyan jami’an kasar game da batutuwan da suka jibanci farfado da hadin gwiwar sassan biyu kan batun sauyin yanayi.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Bi Ra’ayinta Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Ko shakka babu, alakar Sin da Amurka na da matukar muhimmanci, da tasiri ga kyautatuwar rayuwar al’ummunsu, da ma na sauran kasashen duniya baki daya, kamar dai yadda jami’an sassan biyu suka sha jaddadawa.

To sai dai kuma, kamar yadda muka sha gani, akwai ’yan siyasar Amurka da dama dake siyasantar da alakar kasarsu da Sin, suna yunkurin gurbata tarihin dangantaka, da gurgunta cudanyar Amurka da Sin. Irin wadannan ’yan siyasa burinsu shi ne lahanta moriyar kasar Sin, ta hanyar shafawa kasar bakin fenti.

Lallai yunkurin irin wadannan ’yan siyasa marasa hangen nesa, na iya yin tasiri ga tunanin Amurkawa da dama, wanda hakan ka iya haifar da kyama, ko kin jinin Sin a cikin gida, matakin da ka iya yin tarnaki ga warware sabanin ra’ayi ko mahangar kasashen biyu cikin sauki. La’akari da haka, muna iya cewa, irin wadannan ’yan siyasa na haifar da babbar illa ga alakar Sin da Amurka, maimakon su zamo wakilai na gari masu kokarin dinke baraka.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Bisa kimar alakar Sin da Amurka, da tasirinta ga ci gaban harkokin kasa da kasa, ya dace a yi watsi da ra’ayin tsirarun ’yan siyasar Amurka, masu kokarin gurgunta tafiya mai kyau tsakanin kasashen biyu. Kuma hanyar yin hakan ita ce Amurka ta nacewa biyayya ga ka’idoji, da sanarwar hadin gwiwa uku da shugabannin kasashen biyu suka amincewa, kana Amurkan ta daina tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin, kuma sassan biyu su ci gaba da tuntubar juna, bisa martaba moriyar juna, da kiyaye kimar manyan batutuwan dake jan hankalin su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Yi Mamakin Rashin Nasara A Hannun Arsenal -Xavi

Next Post

Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes

Related

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

2 hours ago
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

3 hours ago
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden
Daga Birnin Sin

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

4 hours ago
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

5 hours ago
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

7 hours ago
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021
Daga Birnin Sin

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

7 hours ago
Next Post
Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes

Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.