• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Dama Ce Ta Bunkasar Duniya

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasar Sin Dama Ce Ta Bunkasar Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumomin kasa da kasa na ci gaba da bayyana kyakkyawan fatansu ga karkon da tattalin arzikin kasar Sin ke da shi, tare da bayyana hasashen ci gaban hakan a shekaru dake tare, suna masu bayyana imanin su ga manyan nasarorin da Sin din ke samu ta fuskar fadadar cinikayya, da kere-keren masanaantu, da daidaito a alkaluman raya tattalin arziki. Ko shakka babu, hakan na kara sanyawa sassan kasa da kasa kara jin karfin gwiwa game da tattalin arzikin Sin.

A tsawon shekaru, kasar Sin na ta daukar matakan dunkulewa, da kara kaimin farfado da tattalin arziki, da samar da sabbin damammaki ga kasashen duniya, musamman masu tasowa ta fuskar ingiza bunkasuwa tare, karkashin shirye-shirye daban daban, irin su dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka ko FOCAC, da shawarar “ziri daya da hanya daya” da sauran su, ta yadda za a kai ga samar da duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil adama.

  • Rikicin Ƴan daba Yayi Sanadin mutuwar mutum 1, Da Raunata 2 A Kano
  • ASUU Ta Bada Wa’adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki

Hukumomi da cibiyoyin hada-hadar kudade na duniya, irin su bankin samar da ci gaba na Asiya, da Goldman Sachs, da Morgan Stanley da sauran su, duk sun daga mizanin hasashen da suka yi na ci gaban tattalin arzikin Sin a shekarar nan ta 2024. Hakan kuma manuniya ce ga yadda Sin din ta zamo muhimmiyar mai samar da daidaito, da ingiza bunkasar tattalin arzikin duniya.

A zahiri take cewa Sin ta taka muhimmiyar rawa, wajen samar da hajoji bisa kyakkyawan farashi ga kasuwannin duniya a matsayinta na babbar cibiyar masanaantu. Tana kuma fadada shigo da hajojin sauran kasashe zuwa babbar kasuwarta mai dinbin jamaa. Kaza lika, matakin Sin na kara bude kofa, da gudanar da sauye-sauye masu inganci, sun kara fadada cudanyarta, da cin gajiya tare da sauran sassan kasa da kasa.

Yayin da Sin ke kara bude kofa ga waje, a daya bangaren tana kara zamanantar da kanta karkashin manufofin samar da ci gaba mai nagarta, inda masharhanta da dama ke ganin babbar kasuwar kasar mai yawan alumma da ta kai sama da biliyan 1.4, za ta ci gaba da bude sabbin babuka na ci gaba da kara farfadowa.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Duniya na kara shaida yadda kasar Sin ke ci gaba da raba damammakinta tare da sauran kasashe, ta yadda za a kai ga samun ci gaba mai dorewa, da nasarar dukkanin manufofin gina alummar duniya mai cin gajiyar hadin gwiwar bai daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bunkasar SinJapanKasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Bai Wa ‘Yansanda Umarnin Fitar Da Aminu Ado Daga Fadar Nassarawa 

Next Post

Ya Kamata A Karfafa Manufar Amfani Da Harsunan Gado A Makarantu

Related

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

2 hours ago
Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

20 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

21 hours ago
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

22 hours ago
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma
Daga Birnin Sin

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

23 hours ago
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
Daga Birnin Sin

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

24 hours ago
Next Post
Ya Kamata A Karfafa Manufar Amfani Da Harsunan Gado A Makarantu

Ya Kamata A Karfafa Manufar Amfani Da Harsunan Gado A Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

July 3, 2025
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

July 3, 2025
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

July 3, 2025
Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

July 3, 2025
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

July 3, 2025
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

July 3, 2025
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

July 3, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

July 3, 2025
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.