Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTON MUSAMMAN

Cikakken Hirar BBC Da Kakakin Buhari Kan Ta’asar Da Beraye Suka Yi A Ofishin Buhari

by Tayo Adelaja
August 25, 2017
in RAHOTON MUSAMMAN
3 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya

Shugaban Nijeriya Muhamadu Buhari zai shafe wata uku yana aiki daga gidansa, bayan ya shafe wasu wata ukun yana jinya a Landan. Wani Kakakin fadar Gwamnatin ne ya ce  Beraye ne suka mamaye ofishin shugaban. lokacin da yake Landan, kuma suka lalata na’urar sanyaya daki. Shugaba Buhari ya sha suka a shafukan sada zumunta game da kin bada karin haske kan rashin lafiyar tasa, a jawabin da yayi ga al’umman Nijeriya a ranar litinin.

samndaads

Ga hirar BBC kamar haka da:

GARBA SHEHU: Na farko ina son na yi jawabi cewar shugaban Nijeriya yana da ofis guda biyu a cikin nan fadar gwamnatin tarayya. Shuwagabanin da duk aka yi a baya nan Nijeriya, sukan yi amfani da wancan ofis ko kuma wannan ofis.

GARBA SHEHU: Mun dai cika bayan cewa a tarihin mulkin fadar shugaban kasar Nijeriya, shugaba Abacha shekarun da yayi yana mulki a wancan ofis na gida yake aiki. Sabili da haka wannan lalura ta kawo haka. kamar misali kwana dari 100 da ba a amfani da ofis sabili da haka a kulle yake, yayin da baya nan KWARI da BERAYE da sauransu sun damejin wayoyi na Air conditioner (na’urar sanyaya daki) har da Carpet da sauransu suka yayyaga.

BBC: Dukka kusan fiye da watanni ukun da ya kwashe a can ba a gano da wannan barnar ba sai da ya dawo?

GARBA SHEHU: Lokacin da aka gano an bude ofishin, inda aka ce idan zai dawo sai a bude a karkade a gyara sai aka ga wannan barnar. Kamfanin Julius Berger yanzu haka su ke aiki a ofishinsa. Su karkade duk wani barna da aka yi su gyata, in ma wani abu ake so a canza sai a canza.

BBC: Kamar tsawon watanni ukun da aka yi ba a taba tunanin a leka tun da idan waje na rufe an san za a samu kura ko dan wasu tarkacen kwari ba. to meye sa da ya tafi, lokacin da zai dawo ba a shiga an gyara ba tun da an san in ya dawo zai koma ofis?

GARBA SHEHU: Maganar da ake yi shi ne san da zai dawo lokacin ne za a bude ofis a karkadeshi a gyara. Ai sai da dalili, kuma kai waye kai? Da zaka zo ka ce a bude maka ofishin shugaban kasa kawai ka je ka duba?

BBC: Tsawon wani lokacin zaka dauka ana wannan gyara?

GARBA SHEHU: Yauwa to ina son ku tambayi kamfanin Julius Berger ku ji domin su suka zo suka kiddige aikin da ake bukata za a yi, su kuma aka ce su zo su yi wannan gyarar.

GARBA SHEHU: Ni tambaya ce ban yi ba, amma su da suke kwangilar sun san iya lokacin da zai dauka.

BBC: Wannan shi ne kamar karo na biyu da aka ce zai ke ringa aiki daga gida a maimakon ofis, shin baka ganin ko har zuwa yanzu bai samu karfin da zai iya zuwa ofis ya yi aiki sai yake yi daga gida?

GARBA SHEHU: Ai duk wanda ya ga shugaba Muhammadu Buhari ai ba zai yi wannan maganar ba. amma ita siyasa ta Nijeriya ai haka ta gada.

BBC: Kana ganin daga gidan zai ke aikin da suka kamata yayi kamar yanda zai yi a ofis na waje?

GARBA SHEHU: A!! Ba abun da zai rage yanzu haka da ne ke yi miki magana, dukkanin shuwagabanin sassa daban-daban na tsaro na kasar nan suna tare da shi suna ganawa.

BBC: To da yake ga shi ya dawo ya fara aiki kamar da me zai fara?

GARBA SHEHU: Da tattaunawa da shuwagabinin sassa daban-daban. Yau kuma hankalinsa ya karkata wajen harkar tsaro ta kasa.

BBC: A jawabin da yayi a ranar litinin da safe ana maganar bai yi magana kan tattalin arziki ba?

GARBA SHEHU: Dama jawabin ba a ce za a yi jawabin da zai kunshi komai da komai ba; shi shugaba Muhammadu Buhari zaman lafiya da tsaron kasa ya kankama kafin a zo a tattauna kan wasu abubuwan.

BBC: Malam Garba Shehu kenan mai baiwa shugaban Nijeriya shawara akan harkokin yada labarai.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Ziyarar Da Shugabannin PDP Da APC Suka Kai Wa Shugaba Buhari Yau

Next Post

Hukumar Jin Dadin Alhazan Jihar Bauchi Suna Tsaka-Mai-Wuya

RelatedPosts

JIBWIS-FCT

Kwamitin Tallafa Wa Marayu Na JIBWIS-FCT Ya Gudanar Da Taron Karshen Shekara

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Kwamitin tallafawa marayu na Jama’atu Izalatul Bid’a Wa’ikamatis Sunnah dake...

Sana’ar Mazarkwaila

Yadda Sana’ar Mazarkwaila Ta Sauya Daga Rawar Doki Zuwa Rawar Babur

by Sulaiman Ibrahim
1 week ago
0

Mai karatu, yau alkalaminmu zai duba wani sashe ne na...

Hanyar Abuja-Kaduna

Tabbatar Da Tsaro: NAF Ta Gundunar Da Gagarumin Atisaye A Hanyar Abuja-Kaduna

by Sulaiman Ibrahim
3 weeks ago
0

A ci gaba da kokarin da ta ke yi na...

Next Post

Hukumar Jin Dadin Alhazan Jihar Bauchi Suna Tsaka-Mai-Wuya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version