• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa Ƙungiyar ‘Yan Kasuwar Man Fetur Masu Zaman Kansu (IPMAN) bisa namijin ƙoƙarin da suke yi na ganin an fito da tsarin samar da makamashi na wanda Ba man fetur ba da Gwamnatin Tarayya ta ɓullo da shi bayan cire tallafin man fetur da Shugaba Bola Tinubu ya yi.

Idris, wanda ya bayyana hakan a lokacin da ya karɓi baƙuncin kwamitin gudanarwa na IPMAN na ƙasa a ofishinsa da ke Abuja a ranar Alhamis don ziyarar ban-girma, ya ce Gwamnatin Tarayya na da burin rage farashin sufuri da sama da kashi 50 cikin ɗari ta hanyar shirin amfani da motoci masu aiki da iskar gas (CNG Initiative).

  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Kai Don Ciyar Da Jihar Gaba
  • ‘Yan Sandan Sin Sun Kama Tan 25.9 Na Miyagun Kwayoyi A Shekarar 2023

“Bayan cire tallafin man fetur, ba shakka ana tsammanin farashin man fetur zai hauhawa. Hakan kuma zai shafi farashin sufurin da ‘yan Nijeriya ke kaiwa da komowa a wuraren ayyukansu daban-daban.

“Nan da nan Gwamnatin Tarayya ta yi tunanin cewa ya kamata, ban da wasu matakan, ta ɓullo da CNG. Ana sa ran CNG zai rage farashin sufuri da sama da kashi 50 cikin ɗari, kuma ina farin cikin cewa IPMAN na kan gaba wajen ganin an cimma nasarar shirin CNG ɗin,” inji shi.

Ministan ya ce matakin da Shugaba Tinubu ya ɗauka na cire tallafin man fetur ya ba da dama ta musamman ga ƙungiyoyi irin su IPMAN da za su kasance kan gaba wajen tsara yanayin makamashi a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

Ministan ya ce Nijeriya a matsayinta na ƙasa ta na neman wasu hanyoyin da za ta rage farashin sufuri kuma CNG ita ce hanya mafi inganci da za a bi.

Idris ya ce tuni Gwamnatin Tarayya a matakin farko ta ware naira biliyan 100 domin sayen motocin bas ɗin CNG da kuma kafa cibiyoyin CNG a faɗin ƙasar nan.

Ya ce wannan yana baya ga ɓullo da dokar hana biyan haraji ga masu shigo da kaya na CNG da sauran masu saka hannun jari a wannan ɓangaren.

“Za ku iya tunawa Gwamnatin Tarayya tun farko ta ware naira biliyan 100 don sayen motocin bas na CNG da kuma kafa cibiyoyin CNG a faɗin kasar nan,” inji shi.

Yayin da yake neman goyon bayan ƙungiyar IPMAN ɗin domin samun nasarar shirin Sabuwar Fata na Shugaba Tinubu, ministan ya yi masu godiya bisa la’akari da ma’aikatarsa da ma hukumominta a matsayin amintattun abokan hulɗar su na ƙoƙarin daƙile labaran ƙarya da ake yaɗawa kan ayyukan IPMAN.

Ministan ya koka da yadda labaran ƙarya ke yin illa ga ɓangarori daban-daban na al’umma, ya kuma ce akwai fatan alheri ta hanyar haɗin gwiwar ma’aikatarsa da UNESCO na samar da matakan daƙile illolin labaran ƙarya.

Ya yi alƙawarin ba da ƙarin haske ga shirin cikin gida na ƙungiyar mai taken “IPMAN A Yau”, a kan hukumomin yaɗa labarai daban-daban da ke ƙarƙashin ma’aikatarsa.

Idris ya kuma yi alƙawarin yin amfani da tsarin mambobi 30,000 na IPMAN wajen aiwatar da shirye-shiryen sake daidaita darajar da ke ƙunshe a cikin Yarjejeniyar Ƙimar Kasa.

A nasa jawabin, shugaban ƙungiyar IPMAN, Alhaji Abubakar Maigandi Shettima, ya yi alƙawarin ba da goyon baya ga Shirin CNG na shugaban ƙasa, kuma ya yi alƙawarin bai wa gwamnati haɗin kai a cikin shirin samar da makamashin da ba fetur ba, wanda zai ba da ƙwarin gwiwa wajen tabbatar da ajandar Sabuwar Fata ta shugaban ƙasa.

Ya koka kan yadda a kullum ake sarrafa farashin man fetur ta hanyar yaɗa labaran ƙarya tare da neman goyon bayan ma’aikatar domin yaƙar wannan barazana.

Shettima ya ce a nasu ɓangaren, IPMAN ta fito da wani shiri mai taken “IPMAN A Yau” – shirin rediyo da talabijin, wanda zai zama tushen labarai na gaskiya kan ayyukan ƙungiyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cire Tallafin feturGwamnatin shugaba TinubuTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Tana Murnar Mummunar Ribar Da Ta Ci

Next Post

Kamfanonin Ketare Dake Kasar Sin Sun Amince Da Makomar Tattalin Arzikinta

Related

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas
Labarai

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

7 hours ago
Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan
Labarai

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

8 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Labarai

Hatsarin Jirgi: Babu Batun Zagon-ƙasa Ga Harkokin Sufurin Jiragen Ƙasan Abuja-Kaduna – Gwamnati

13 hours ago
Kwale-kwale
Labarai

Haɗarin Kwale-kwale Ya Ci Rayukan Mutane 15 A Zamfara

14 hours ago
Sin Za Ta Kare Moriyarta Ta Hanyar Mayar Da Martani Game Da Sabon Matakin Kakaba Harajin Kwastan Da Amurka Ke Dauka
Labarai

Trump Ya Kakaba Kashi 50 Kan Indiya Saboda Sayen Kaya Daga Rasha

14 hours ago
An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 
Manyan Labarai

An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 

15 hours ago
Next Post
Kamfanonin Ketare Dake Kasar Sin Sun Amince Da Makomar Tattalin Arzikinta

Kamfanonin Ketare Dake Kasar Sin Sun Amince Da Makomar Tattalin Arzikinta

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

August 31, 2025
Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

August 31, 2025
Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

August 31, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

August 31, 2025
Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

August 31, 2025
Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

August 31, 2025
Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

August 31, 2025
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

August 31, 2025
Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

August 31, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgi: Babu Batun Zagon-ƙasa Ga Harkokin Sufurin Jiragen Ƙasan Abuja-Kaduna – Gwamnati

August 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.