• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa Ƙungiyar ‘Yan Kasuwar Man Fetur Masu Zaman Kansu (IPMAN) bisa namijin ƙoƙarin da suke yi na ganin an fito da tsarin samar da makamashi na wanda Ba man fetur ba da Gwamnatin Tarayya ta ɓullo da shi bayan cire tallafin man fetur da Shugaba Bola Tinubu ya yi.

Idris, wanda ya bayyana hakan a lokacin da ya karɓi baƙuncin kwamitin gudanarwa na IPMAN na ƙasa a ofishinsa da ke Abuja a ranar Alhamis don ziyarar ban-girma, ya ce Gwamnatin Tarayya na da burin rage farashin sufuri da sama da kashi 50 cikin ɗari ta hanyar shirin amfani da motoci masu aiki da iskar gas (CNG Initiative).

  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Kai Don Ciyar Da Jihar Gaba
  • ‘Yan Sandan Sin Sun Kama Tan 25.9 Na Miyagun Kwayoyi A Shekarar 2023

“Bayan cire tallafin man fetur, ba shakka ana tsammanin farashin man fetur zai hauhawa. Hakan kuma zai shafi farashin sufurin da ‘yan Nijeriya ke kaiwa da komowa a wuraren ayyukansu daban-daban.

“Nan da nan Gwamnatin Tarayya ta yi tunanin cewa ya kamata, ban da wasu matakan, ta ɓullo da CNG. Ana sa ran CNG zai rage farashin sufuri da sama da kashi 50 cikin ɗari, kuma ina farin cikin cewa IPMAN na kan gaba wajen ganin an cimma nasarar shirin CNG ɗin,” inji shi.

Ministan ya ce matakin da Shugaba Tinubu ya ɗauka na cire tallafin man fetur ya ba da dama ta musamman ga ƙungiyoyi irin su IPMAN da za su kasance kan gaba wajen tsara yanayin makamashi a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Ministan ya ce Nijeriya a matsayinta na ƙasa ta na neman wasu hanyoyin da za ta rage farashin sufuri kuma CNG ita ce hanya mafi inganci da za a bi.

Idris ya ce tuni Gwamnatin Tarayya a matakin farko ta ware naira biliyan 100 domin sayen motocin bas ɗin CNG da kuma kafa cibiyoyin CNG a faɗin ƙasar nan.

Ya ce wannan yana baya ga ɓullo da dokar hana biyan haraji ga masu shigo da kaya na CNG da sauran masu saka hannun jari a wannan ɓangaren.

“Za ku iya tunawa Gwamnatin Tarayya tun farko ta ware naira biliyan 100 don sayen motocin bas na CNG da kuma kafa cibiyoyin CNG a faɗin kasar nan,” inji shi.

Yayin da yake neman goyon bayan ƙungiyar IPMAN ɗin domin samun nasarar shirin Sabuwar Fata na Shugaba Tinubu, ministan ya yi masu godiya bisa la’akari da ma’aikatarsa da ma hukumominta a matsayin amintattun abokan hulɗar su na ƙoƙarin daƙile labaran ƙarya da ake yaɗawa kan ayyukan IPMAN.

Ministan ya koka da yadda labaran ƙarya ke yin illa ga ɓangarori daban-daban na al’umma, ya kuma ce akwai fatan alheri ta hanyar haɗin gwiwar ma’aikatarsa da UNESCO na samar da matakan daƙile illolin labaran ƙarya.

Ya yi alƙawarin ba da ƙarin haske ga shirin cikin gida na ƙungiyar mai taken “IPMAN A Yau”, a kan hukumomin yaɗa labarai daban-daban da ke ƙarƙashin ma’aikatarsa.

Idris ya kuma yi alƙawarin yin amfani da tsarin mambobi 30,000 na IPMAN wajen aiwatar da shirye-shiryen sake daidaita darajar da ke ƙunshe a cikin Yarjejeniyar Ƙimar Kasa.

A nasa jawabin, shugaban ƙungiyar IPMAN, Alhaji Abubakar Maigandi Shettima, ya yi alƙawarin ba da goyon baya ga Shirin CNG na shugaban ƙasa, kuma ya yi alƙawarin bai wa gwamnati haɗin kai a cikin shirin samar da makamashin da ba fetur ba, wanda zai ba da ƙwarin gwiwa wajen tabbatar da ajandar Sabuwar Fata ta shugaban ƙasa.

Ya koka kan yadda a kullum ake sarrafa farashin man fetur ta hanyar yaɗa labaran ƙarya tare da neman goyon bayan ma’aikatar domin yaƙar wannan barazana.

Shettima ya ce a nasu ɓangaren, IPMAN ta fito da wani shiri mai taken “IPMAN A Yau” – shirin rediyo da talabijin, wanda zai zama tushen labarai na gaskiya kan ayyukan ƙungiyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cire Tallafin feturGwamnatin shugaba TinubuTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Tana Murnar Mummunar Ribar Da Ta Ci

Next Post

Kamfanonin Ketare Dake Kasar Sin Sun Amince Da Makomar Tattalin Arzikinta

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

13 minutes ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

4 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

5 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

6 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

8 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

11 hours ago
Next Post
Kamfanonin Ketare Dake Kasar Sin Sun Amince Da Makomar Tattalin Arzikinta

Kamfanonin Ketare Dake Kasar Sin Sun Amince Da Makomar Tattalin Arzikinta

LABARAI MASU NASABA

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.