• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cittar Da Ake Fitarwa kasashen Waje Ta Ragu Da Kashi 74 Cikin 100

by Abubakar Abba
7 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Cittar Da Ake Fitarwa kasashen Waje Ta Ragu Da Kashi 74 Cikin 100
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kididdiga da aka fitar a hukumance ta tabbatar da cewa, shekarar 2024, a cikin wata tara; Cittar da ake nomawa tare da fitar da ita daga Nijeriya zuwa kasuwannin duniyua, ta ragu da kashi 74 cikin 100, sakamakon cutar da ta lalata gonakinta a fadin kasar.

A cewar Hukumar kiddiga ta kasa (NBS), wasu bayanai na kasuwancin katare ya nuna cewa, Cittar da Nijeriya ke fitarwa waje ta ragu da kashi 74 cikin 100, wadda kudinta a shekarar 2024, ya ragu zuwa Naira biliyan 6.28, sabanin Naira biliyan 23.76 2023 da ake samu a baya.

  • Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida
  • Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

Haka zalika, faduwar darajar Naira zuwa 1,500 a kan kowace Dala a 2024, ya kara haifar da matsalar; wanda kamata ya yi a ce, kimar Cittar ta karu a 2023; amma sai dai cutar ta yi mata illa a gonakin da aka shuka ta, hakan ya jawo raguwar fitar da ita kasashen ketare.

Kazalika, wasu kwararru a fannin; sun yi nuni da cewa, kimar Cittar zai ci gaba da raguwa a wannan shekara ta 2025, saboda Cibiyoyin bincike kan amfanin gona a kasar, sun gaza lalubo da mafitar dakile yaduwar cutar.

Cittar dai, na daya daga cikin jerin amfanin gonar da gwamnatin taryya ta tsara za su kara bunkasa tattalin arzikin kasar da kuma kara mayar da hankali wajen fitar da ita kasashen ketare.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

 

dimbin Asarar Da Manoman Cittta Suka Tabka:

Shugabar kungiyar manoman Citta da sarrafata ta kasa (GGPMAN) Florence Edwards, ta alakanta samun raguwar Cittar da ake fitarwa daga kasar nan zuwa kasashen ketare da barkewar cutar da ta lalata gonakin wasu manomanta.

Florence ta kara da cewa, akasarin irin samfurin Cittar da manoman ke shukawa a fadin kasar nan, sun shafe sama da shekaru 20 suna amfani da shi.

Ita ma wata manomiyar Cittar a Jihar Kaduna, Joy Bolus ta bayyana cewa, ta kashe sama da Naira miliyan daya a shekarar da ta gabata wajen aikin noman Cittar a tata gonar, ta hanyar yin hadaka da miinta, amma saboda barkewar cutar a bara, hakan ya jawo gonar ta lalace baki-daya.

“A kakar noman bara, ni da mijina mun yi asarar sama da Naira 800, 000, bayan barkewar cutar”, a cewar Joy.

Duk kokarin da gwamnatin tarayya ta yi na magance yaduwar cutar, hakan bai samar da wani sakamako na a zo a gani ba, musamman ganin yadda manomanta a Jihohin Kaduna, Kano da wasu yankuna biyu na kasar da aka fi yin noman ke ci gaba da kirgar irn asarar da suka tabka sakamakon barkewar cutar.

karamin Ministan Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sabi Abdullahi ya bayyana cewa, tun bayan barkewar cutar a 2023, manoman da annobar cutar ta afkawa a gonakinsu, sun yi asarar kimanin Naira biliyan 12.

A watan Oktoban 2023, gwamnatin tarayya; ta samar wa da manoman, musamman na jihohin da aka fi yin nomanta tallafin Naira biliyan 1.6 tare kuma da raba musu magungunan feshin cutar, domin rage musu radadin annobar.

Jaridar BusinessDay, tun da farko ta ruwaito cewa, farashin Cittar ya karu da rubi shida a shekaru biyu da suka gabata, inda kowane buhunta daya a 2023 ya kai Naira 50, 000, sannan kuma ya karu zuwa Naira 300,000 a shekarar 2025.

Wasu manoman, sun alakanta hauhawar farashin da barkewar cutar a 2023, inda hakan ya jawo wa manoman nata yin asarar kimanin Naira biliyan 12.

A cikin kasafin kudi na 2025, an kara wa Hukumar Samar da Ingantaccen Irin Noma ta kasa (NASC) kashi 36, kimanin Naira biliyan 3.8, sabanin Naira biliyan 2.8 da aka ware mata a kasafin kudi na 2024, amma abin takaici; har yanzu manoman kasar, ba su iya samun ingantaccen Irin ba.

A cewar Hukumar Samar Wadattacen Abinci da Bunkasa Aikin Noma (FAO) ta duniya ta ce, a fidin duniya kaf; Nijeriya na daya daga cikin kasashen da ke kan gaba wajen noman Citta, duba da yadda kasar ta noma kimanin tan 781,000 a 2023.

Mafi akasari, Nijeriya na fitar da Cittar da aka noma a kasar ne zuwa kasuwannin Gabas ta Tsakiya ko kuma Nahiyar Turai.

“Manoman Citttar, na bukatar samar musu da Irinta, mai bijer wa kowace irin cutar da ke yi wa gonakinsu illa tare kuma da yin gwajin kasar da ake noma ta, don gano inda cutar ke fara kunno kai”, in ji Florence.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CittaGona
ShareTweetSendShare
Previous Post

Thomas Bach: Kasar Sin Ta Ba Da Gagarumar Gudummawa Ga Bunkasa Wasannin Olympics

Next Post

Sin: Manufar Zuba Jarin Amurka Na Matukar Kassara Hadin Gwiwar Kasuwancin Kamfanonin Sin Da Amurka

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

9 hours ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

3 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

3 weeks ago
Next Post
Sin: Manufar Zuba Jarin Amurka Na Matukar Kassara Hadin Gwiwar Kasuwancin Kamfanonin Sin Da Amurka

Sin: Manufar Zuba Jarin Amurka Na Matukar Kassara Hadin Gwiwar Kasuwancin Kamfanonin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.