ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cittar Da Ake Fitarwa kasashen Waje Ta Ragu Da Kashi 74 Cikin 100

by Abubakar Abba
1 year ago
Citta

Wata kididdiga da aka fitar a hukumance ta tabbatar da cewa, shekarar 2024, a cikin wata tara; Cittar da ake nomawa tare da fitar da ita daga Nijeriya zuwa kasuwannin duniyua, ta ragu da kashi 74 cikin 100, sakamakon cutar da ta lalata gonakinta a fadin kasar.

A cewar Hukumar kiddiga ta kasa (NBS), wasu bayanai na kasuwancin katare ya nuna cewa, Cittar da Nijeriya ke fitarwa waje ta ragu da kashi 74 cikin 100, wadda kudinta a shekarar 2024, ya ragu zuwa Naira biliyan 6.28, sabanin Naira biliyan 23.76 2023 da ake samu a baya.

  • Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida
  • Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

Haka zalika, faduwar darajar Naira zuwa 1,500 a kan kowace Dala a 2024, ya kara haifar da matsalar; wanda kamata ya yi a ce, kimar Cittar ta karu a 2023; amma sai dai cutar ta yi mata illa a gonakin da aka shuka ta, hakan ya jawo raguwar fitar da ita kasashen ketare.

ADVERTISEMENT

Kazalika, wasu kwararru a fannin; sun yi nuni da cewa, kimar Cittar zai ci gaba da raguwa a wannan shekara ta 2025, saboda Cibiyoyin bincike kan amfanin gona a kasar, sun gaza lalubo da mafitar dakile yaduwar cutar.

Cittar dai, na daya daga cikin jerin amfanin gonar da gwamnatin taryya ta tsara za su kara bunkasa tattalin arzikin kasar da kuma kara mayar da hankali wajen fitar da ita kasashen ketare.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

 

dimbin Asarar Da Manoman Cittta Suka Tabka:

Shugabar kungiyar manoman Citta da sarrafata ta kasa (GGPMAN) Florence Edwards, ta alakanta samun raguwar Cittar da ake fitarwa daga kasar nan zuwa kasashen ketare da barkewar cutar da ta lalata gonakin wasu manomanta.

Florence ta kara da cewa, akasarin irin samfurin Cittar da manoman ke shukawa a fadin kasar nan, sun shafe sama da shekaru 20 suna amfani da shi.

Ita ma wata manomiyar Cittar a Jihar Kaduna, Joy Bolus ta bayyana cewa, ta kashe sama da Naira miliyan daya a shekarar da ta gabata wajen aikin noman Cittar a tata gonar, ta hanyar yin hadaka da miinta, amma saboda barkewar cutar a bara, hakan ya jawo gonar ta lalace baki-daya.

“A kakar noman bara, ni da mijina mun yi asarar sama da Naira 800, 000, bayan barkewar cutar”, a cewar Joy.

Duk kokarin da gwamnatin tarayya ta yi na magance yaduwar cutar, hakan bai samar da wani sakamako na a zo a gani ba, musamman ganin yadda manomanta a Jihohin Kaduna, Kano da wasu yankuna biyu na kasar da aka fi yin noman ke ci gaba da kirgar irn asarar da suka tabka sakamakon barkewar cutar.

karamin Ministan Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sabi Abdullahi ya bayyana cewa, tun bayan barkewar cutar a 2023, manoman da annobar cutar ta afkawa a gonakinsu, sun yi asarar kimanin Naira biliyan 12.

A watan Oktoban 2023, gwamnatin tarayya; ta samar wa da manoman, musamman na jihohin da aka fi yin nomanta tallafin Naira biliyan 1.6 tare kuma da raba musu magungunan feshin cutar, domin rage musu radadin annobar.

Jaridar BusinessDay, tun da farko ta ruwaito cewa, farashin Cittar ya karu da rubi shida a shekaru biyu da suka gabata, inda kowane buhunta daya a 2023 ya kai Naira 50, 000, sannan kuma ya karu zuwa Naira 300,000 a shekarar 2025.

Wasu manoman, sun alakanta hauhawar farashin da barkewar cutar a 2023, inda hakan ya jawo wa manoman nata yin asarar kimanin Naira biliyan 12.

A cikin kasafin kudi na 2025, an kara wa Hukumar Samar da Ingantaccen Irin Noma ta kasa (NASC) kashi 36, kimanin Naira biliyan 3.8, sabanin Naira biliyan 2.8 da aka ware mata a kasafin kudi na 2024, amma abin takaici; har yanzu manoman kasar, ba su iya samun ingantaccen Irin ba.

A cewar Hukumar Samar Wadattacen Abinci da Bunkasa Aikin Noma (FAO) ta duniya ta ce, a fidin duniya kaf; Nijeriya na daya daga cikin kasashen da ke kan gaba wajen noman Citta, duba da yadda kasar ta noma kimanin tan 781,000 a 2023.

Mafi akasari, Nijeriya na fitar da Cittar da aka noma a kasar ne zuwa kasuwannin Gabas ta Tsakiya ko kuma Nahiyar Turai.

“Manoman Citttar, na bukatar samar musu da Irinta, mai bijer wa kowace irin cutar da ke yi wa gonakinsu illa tare kuma da yin gwajin kasar da ake noma ta, don gano inda cutar ke fara kunno kai”, in ji Florence.

Citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Sin: Manufar Zuba Jarin Amurka Na Matukar Kassara Hadin Gwiwar Kasuwancin Kamfanonin Sin Da Amurka

Sin: Manufar Zuba Jarin Amurka Na Matukar Kassara Hadin Gwiwar Kasuwancin Kamfanonin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.