ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida

by Abubakar Abba
1 year ago
Citta

Bullar cutar da ke lalata Citta, ya sa farashinta ya karu har sau shida; cikin shekaru biyu kacal, ana sayar da duk buhu guda a kan Naira 50,000 a 2023, inda yanzu kuma farashin ya tashi zuwa Naira 300,000.

Manoman cittar, sun alakanta karin farashinta nata, sakamakon bullar wannan mummunar cuta da ke harbin ta ‘Blight’, wadda ta bulla a   2023, ta kuma jawo wa manoman asarar kimanin Naira biliyan 12.

  • Nazarin CGTN: Tsauraran Manufofin Amurka Na Shan Suka
  • Asibitin Aminu Kano Ya Musanta Cire Mahaifar Mara Lafiya Ba Tare Da Izini Ba

Ita dai wannan cuta, tana harbin jijiyar Cittar da aka shuka ne, sannan kuma tana yaduwa zuwa sauran sassan jikinta.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, wannan mummunar cuta, ba karamar illa take yi wa gonakin da ake yin noman wannan Citta ba, musamman a Jihar Kaduna da wasu sauran jihohin wannan kasa, wanda hakan ya yi sanadiyar sama da kashi 90 na gonakin tabka mummunar asara.

Jihar Kaduna dai, ta kasance kan gaba wajen noman Citta a fadin Nijeriya baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Wata manomiyar wannan Citta, mai suna Joy Bauna da ke Karamar Hukumar Jema’a ta Jihar Kaduna, ta koka kan irin asarar da ta tabka sakamakon wannan annobar, inda ta sanar da cewa, “Cutar ta lalata mana daukacin Cittar da muka shuka, domin kuwa duk ta rube, inda na yi asarar sama da Naira 200,000.”

“Na gaza sake yin wani noman a 2024, domin kuwa ba ni da ingantaccen Irin da zan sake shukawa”,  in ji Joy.

“Wasu daga cikinmu, ba su samu wani taimako daga wurin gwamnati ba, wanda hakan ya sa muka gaza sake yin wani noman, idan har fadin da ake yi na cewa, duk farashin buhu guda yanzu ya kai Naira 300,000, babu shakka lamarin ya munana, sai dai idan gwamnati ta taimaka mana da Iri, musamman mu kananan manoma, wannan ne zai ba mu damar sake yin wani noman a kakar bana”, a cewar Joy.

Karamin Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi ya sanar da cewa, a 2023 bayan bullar wannan cuta, manoma sun yi asarar kudi kimanin Naira biliyan 12.

Ya bayyana cewa, manoman da suka yi inshorar amfanin ne kadai, suka samu kudin dauki daga kamfanonin inshorar.

Hukumar Kula da Samar da Abinci ta Duniya (FOA) ta bayyana cewa, Nijeriya ce kan gaba wajen noman Citta a duniya, domin kuwa tana noma Cittar da yawanta ya kai kimanin tan 523,000 a duk shekara.

Kazalika, Hukumar Kula da Fitar da Kaya zuwa kasashen waje (NEPC) ta sanar da cewa, Nijeriya na da kashi 14 cikin 100 a kasuwar duniya na yawan Cittar da ake hada-hadar kasuwancinta.

“Ana fitar da kimanin kashi 90 a cikin 100 na wannan Citta, domin kuwa wadda ake nomawa a kasar nan, ta sha ban-ban da sauran wadda ake nomawa a sauran kasashe, sakamakon irin kyan da take da shi”, in ji NEPC.

Babban Shugaba, kuma Babban Sakare na Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa (NADF), Mohammed Ibrahim ya bayyana cewa, a lokacin da cutar ta bulla a 2023, kimanin manoma 5,000 da ke kanannan hukumomi bakwai na Jihar Kaduna, gwamnatin tarayyya ta taimakawa da kayan noman Cittar a 2023.

Ya ce, kananan hukumomin sun hada da; Kachia, Zango-Kataf, Kaura, Kagarko, Jema’a, Jabba da kuma Sanga.

“Duk a cikin daukin bayar da kudi, gidauniyar ta NADF ta kuma taimaka wa Masa’antar Sarrafa Citta, ta ‘Illaj Ginger Factory’ da ke Jihar Kaduna, wanda hakan na daya daga cikin kokarin shirin farfado da nomanta a fadin wannan kasa”, in ji Ibrahim.

Kazalika ya sanar da cewa, an kuma kaddamar da shirin dakile yaduwar cutar, ta hanyar kirkiro da Jami’an GBECT.

Citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.