ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida

by Abubakar Abba
1 year ago
Citta

Bullar cutar da ke lalata Citta, ya sa farashinta ya karu har sau shida; cikin shekaru biyu kacal, ana sayar da duk buhu guda a kan Naira 50,000 a 2023, inda yanzu kuma farashin ya tashi zuwa Naira 300,000.

Manoman cittar, sun alakanta karin farashinta nata, sakamakon bullar wannan mummunar cuta da ke harbin ta ‘Blight’, wadda ta bulla a   2023, ta kuma jawo wa manoman asarar kimanin Naira biliyan 12.

  • Nazarin CGTN: Tsauraran Manufofin Amurka Na Shan Suka
  • Asibitin Aminu Kano Ya Musanta Cire Mahaifar Mara Lafiya Ba Tare Da Izini Ba

Ita dai wannan cuta, tana harbin jijiyar Cittar da aka shuka ne, sannan kuma tana yaduwa zuwa sauran sassan jikinta.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, wannan mummunar cuta, ba karamar illa take yi wa gonakin da ake yin noman wannan Citta ba, musamman a Jihar Kaduna da wasu sauran jihohin wannan kasa, wanda hakan ya yi sanadiyar sama da kashi 90 na gonakin tabka mummunar asara.

Jihar Kaduna dai, ta kasance kan gaba wajen noman Citta a fadin Nijeriya baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Wata manomiyar wannan Citta, mai suna Joy Bauna da ke Karamar Hukumar Jema’a ta Jihar Kaduna, ta koka kan irin asarar da ta tabka sakamakon wannan annobar, inda ta sanar da cewa, “Cutar ta lalata mana daukacin Cittar da muka shuka, domin kuwa duk ta rube, inda na yi asarar sama da Naira 200,000.”

“Na gaza sake yin wani noman a 2024, domin kuwa ba ni da ingantaccen Irin da zan sake shukawa”,  in ji Joy.

“Wasu daga cikinmu, ba su samu wani taimako daga wurin gwamnati ba, wanda hakan ya sa muka gaza sake yin wani noman, idan har fadin da ake yi na cewa, duk farashin buhu guda yanzu ya kai Naira 300,000, babu shakka lamarin ya munana, sai dai idan gwamnati ta taimaka mana da Iri, musamman mu kananan manoma, wannan ne zai ba mu damar sake yin wani noman a kakar bana”, a cewar Joy.

Karamin Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi ya sanar da cewa, a 2023 bayan bullar wannan cuta, manoma sun yi asarar kudi kimanin Naira biliyan 12.

Ya bayyana cewa, manoman da suka yi inshorar amfanin ne kadai, suka samu kudin dauki daga kamfanonin inshorar.

Hukumar Kula da Samar da Abinci ta Duniya (FOA) ta bayyana cewa, Nijeriya ce kan gaba wajen noman Citta a duniya, domin kuwa tana noma Cittar da yawanta ya kai kimanin tan 523,000 a duk shekara.

Kazalika, Hukumar Kula da Fitar da Kaya zuwa kasashen waje (NEPC) ta sanar da cewa, Nijeriya na da kashi 14 cikin 100 a kasuwar duniya na yawan Cittar da ake hada-hadar kasuwancinta.

“Ana fitar da kimanin kashi 90 a cikin 100 na wannan Citta, domin kuwa wadda ake nomawa a kasar nan, ta sha ban-ban da sauran wadda ake nomawa a sauran kasashe, sakamakon irin kyan da take da shi”, in ji NEPC.

Babban Shugaba, kuma Babban Sakare na Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa (NADF), Mohammed Ibrahim ya bayyana cewa, a lokacin da cutar ta bulla a 2023, kimanin manoma 5,000 da ke kanannan hukumomi bakwai na Jihar Kaduna, gwamnatin tarayyya ta taimakawa da kayan noman Cittar a 2023.

Ya ce, kananan hukumomin sun hada da; Kachia, Zango-Kataf, Kaura, Kagarko, Jema’a, Jabba da kuma Sanga.

“Duk a cikin daukin bayar da kudi, gidauniyar ta NADF ta kuma taimaka wa Masa’antar Sarrafa Citta, ta ‘Illaj Ginger Factory’ da ke Jihar Kaduna, wanda hakan na daya daga cikin kokarin shirin farfado da nomanta a fadin wannan kasa”, in ji Ibrahim.

Kazalika ya sanar da cewa, an kuma kaddamar da shirin dakile yaduwar cutar, ta hanyar kirkiro da Jami’an GBECT.

Citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.