ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida

by Abubakar Abba
2 years ago
Citta

Bullar cutar da ke lalata Citta, ya sa farashinta ya karu har sau shida; cikin shekaru biyu kacal, ana sayar da duk buhu guda a kan Naira 50,000 a 2023, inda yanzu kuma farashin ya tashi zuwa Naira 300,000.

Manoman cittar, sun alakanta karin farashinta nata, sakamakon bullar wannan mummunar cuta da ke harbin ta ‘Blight’, wadda ta bulla a   2023, ta kuma jawo wa manoman asarar kimanin Naira biliyan 12.

  • Nazarin CGTN: Tsauraran Manufofin Amurka Na Shan Suka
  • Asibitin Aminu Kano Ya Musanta Cire Mahaifar Mara Lafiya Ba Tare Da Izini Ba

Ita dai wannan cuta, tana harbin jijiyar Cittar da aka shuka ne, sannan kuma tana yaduwa zuwa sauran sassan jikinta.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, wannan mummunar cuta, ba karamar illa take yi wa gonakin da ake yin noman wannan Citta ba, musamman a Jihar Kaduna da wasu sauran jihohin wannan kasa, wanda hakan ya yi sanadiyar sama da kashi 90 na gonakin tabka mummunar asara.

Jihar Kaduna dai, ta kasance kan gaba wajen noman Citta a fadin Nijeriya baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Wata manomiyar wannan Citta, mai suna Joy Bauna da ke Karamar Hukumar Jema’a ta Jihar Kaduna, ta koka kan irin asarar da ta tabka sakamakon wannan annobar, inda ta sanar da cewa, “Cutar ta lalata mana daukacin Cittar da muka shuka, domin kuwa duk ta rube, inda na yi asarar sama da Naira 200,000.”

“Na gaza sake yin wani noman a 2024, domin kuwa ba ni da ingantaccen Irin da zan sake shukawa”,  in ji Joy.

“Wasu daga cikinmu, ba su samu wani taimako daga wurin gwamnati ba, wanda hakan ya sa muka gaza sake yin wani noman, idan har fadin da ake yi na cewa, duk farashin buhu guda yanzu ya kai Naira 300,000, babu shakka lamarin ya munana, sai dai idan gwamnati ta taimaka mana da Iri, musamman mu kananan manoma, wannan ne zai ba mu damar sake yin wani noman a kakar bana”, a cewar Joy.

Karamin Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi ya sanar da cewa, a 2023 bayan bullar wannan cuta, manoma sun yi asarar kudi kimanin Naira biliyan 12.

Ya bayyana cewa, manoman da suka yi inshorar amfanin ne kadai, suka samu kudin dauki daga kamfanonin inshorar.

Hukumar Kula da Samar da Abinci ta Duniya (FOA) ta bayyana cewa, Nijeriya ce kan gaba wajen noman Citta a duniya, domin kuwa tana noma Cittar da yawanta ya kai kimanin tan 523,000 a duk shekara.

Kazalika, Hukumar Kula da Fitar da Kaya zuwa kasashen waje (NEPC) ta sanar da cewa, Nijeriya na da kashi 14 cikin 100 a kasuwar duniya na yawan Cittar da ake hada-hadar kasuwancinta.

“Ana fitar da kimanin kashi 90 a cikin 100 na wannan Citta, domin kuwa wadda ake nomawa a kasar nan, ta sha ban-ban da sauran wadda ake nomawa a sauran kasashe, sakamakon irin kyan da take da shi”, in ji NEPC.

Babban Shugaba, kuma Babban Sakare na Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa (NADF), Mohammed Ibrahim ya bayyana cewa, a lokacin da cutar ta bulla a 2023, kimanin manoma 5,000 da ke kanannan hukumomi bakwai na Jihar Kaduna, gwamnatin tarayyya ta taimakawa da kayan noman Cittar a 2023.

Ya ce, kananan hukumomin sun hada da; Kachia, Zango-Kataf, Kaura, Kagarko, Jema’a, Jabba da kuma Sanga.

“Duk a cikin daukin bayar da kudi, gidauniyar ta NADF ta kuma taimaka wa Masa’antar Sarrafa Citta, ta ‘Illaj Ginger Factory’ da ke Jihar Kaduna, wanda hakan na daya daga cikin kokarin shirin farfado da nomanta a fadin wannan kasa”, in ji Ibrahim.

Kazalika ya sanar da cewa, an kuma kaddamar da shirin dakile yaduwar cutar, ta hanyar kirkiro da Jami’an GBECT.

Citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

LABARAI MASU NASABA

Citta

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Citta

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.