• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

City Za Ta Dawo Cikin Hayyacinta Duk Da Rashin Katabus Da Ta Ke Fama Da Shi – Pep Guardiola

by Abba Ibrahim Wada
11 months ago
City

Kocin Manchester City Pep Guardiola ya bayyana cewar har yanzu yana da kwarin gwiwa a kan yan wasansa duk da cewa ya buga wasanni 6 ba tare da samun nasara ba, a baya-bayan nan City ta barar da damarta bayan cin kwallaye uku rigis kuma ta kasa samun nasara a wasan da ta buga da Feyernood a ranar Talata.

Man City ta buga kunnen doki da ci 3-3 da Feyenoord a gasar cin kofin Zakarun Turai duk da cewa a minti na 75 Man City ce kan gaba da kwallaye uku amma kuma Feyernood ta tabbatar da ta samu maki daya a wasan bayan itama ta jefa kwallaye uku a minti 25, da wannan ne

  • Ba Kare Bin Damo Tsakanin Man City Da Arsenal A Etihad 
  • Leicester City Ta Kori Kocinta Bayan Rashin Nasara A Hannun Chelsea 

Manchester City ta buga wasanni shida ba tare da samun nasara ba a dukkan gasar da ta buga.

Guardiola ya ce rashin nasarar da kungiyar ke yi a baya-bayan nan yana shafar kwarin gwiwarsu amma dai duk da haka ba za su bari su barar da damarmakin da suke da su na lashe manyan kofuna a bana ba, mun yi rashin nasara a wasanni da yawa kwanan nan, akwai ‘yan wasanmu da suke fama da rauni kuma suke jinya tsawon lokaci ba tare da sun buga wasanni ba.

Kowa ya san halin da ake ciki, ba lallai ne mu daidaita komai ba dole ne mu ci gaba da atisaye, domin murmurewa sannan mu shirya tunkarar wasannin gaba domin har yanzu muna da damar gyarawa domin fuskantar kalubale,” in ji Guardiola.

LABARAI MASU NASABA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Hakika wannan kaka ta kasance kakar wasa mai wahala a gare mu amma dai kungiyar ta himmatu ga abubuwa da yawa, amma abin takaici wasu abubuwa sun gindaya wanda hakan ya sa muke wahala kuma muke rashin nasara a cewar kocin na Manchester City wanda aka zurawa kungiyarsa kwallaye 17 a wasanni shida da suka buga na baya-bayan nan.

Masu sharhi akan wasannin kwallon kafa sun bayyana rashin katabus din da kungiyar ke fama da shi bai rasa nasaba da raunin da manyan ‘yan wasanta ke fama da shi da suka hada da gwarzon kwallon kafa na Duniya a kakar da ta wuce Rodri Hernandez, Jeremy Doku, Kobacic da sauransu.

Wanda dukkansu suna da rawar da za su taka a City idan aka yi la’akari da yadda dukkan wadannan ‘yan wasan suka taimaka wa City wajen lashe kofin gasar Firimiya a kakar wasannin da ta gabata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana
Wasanni

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars
Wasanni

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta
Labarai

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Next Post
Kano Ta Kaddamar Da Cibiyar Tafi-da-gidanka Ta Farko A Nijeriya Don Yi Wa Motoci Lasisi

Kano Ta Kaddamar Da Cibiyar Tafi-da-gidanka Ta Farko A Nijeriya Don Yi Wa Motoci Lasisi

LABARAI MASU NASABA

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

October 23, 2025
Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

October 23, 2025
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.