• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

City Za Ta Dawo Cikin Hayyacinta Duk Da Rashin Katabus Da Ta Ke Fama Da Shi – Pep Guardiola

by Abba Ibrahim Wada
7 months ago
in Wasanni
0
City Za Ta Dawo Cikin Hayyacinta Duk Da Rashin Katabus Da Ta Ke Fama Da Shi – Pep Guardiola
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kocin Manchester City Pep Guardiola ya bayyana cewar har yanzu yana da kwarin gwiwa a kan yan wasansa duk da cewa ya buga wasanni 6 ba tare da samun nasara ba, a baya-bayan nan City ta barar da damarta bayan cin kwallaye uku rigis kuma ta kasa samun nasara a wasan da ta buga da Feyernood a ranar Talata.

Man City ta buga kunnen doki da ci 3-3 da Feyenoord a gasar cin kofin Zakarun Turai duk da cewa a minti na 75 Man City ce kan gaba da kwallaye uku amma kuma Feyernood ta tabbatar da ta samu maki daya a wasan bayan itama ta jefa kwallaye uku a minti 25, da wannan ne

  • Ba Kare Bin Damo Tsakanin Man City Da Arsenal A Etihad 
  • Leicester City Ta Kori Kocinta Bayan Rashin Nasara A Hannun Chelsea 

Manchester City ta buga wasanni shida ba tare da samun nasara ba a dukkan gasar da ta buga.

Guardiola ya ce rashin nasarar da kungiyar ke yi a baya-bayan nan yana shafar kwarin gwiwarsu amma dai duk da haka ba za su bari su barar da damarmakin da suke da su na lashe manyan kofuna a bana ba, mun yi rashin nasara a wasanni da yawa kwanan nan, akwai ‘yan wasanmu da suke fama da rauni kuma suke jinya tsawon lokaci ba tare da sun buga wasanni ba.

Kowa ya san halin da ake ciki, ba lallai ne mu daidaita komai ba dole ne mu ci gaba da atisaye, domin murmurewa sannan mu shirya tunkarar wasannin gaba domin har yanzu muna da damar gyarawa domin fuskantar kalubale,” in ji Guardiola.

Labarai Masu Nasaba

Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Hakika wannan kaka ta kasance kakar wasa mai wahala a gare mu amma dai kungiyar ta himmatu ga abubuwa da yawa, amma abin takaici wasu abubuwa sun gindaya wanda hakan ya sa muke wahala kuma muke rashin nasara a cewar kocin na Manchester City wanda aka zurawa kungiyarsa kwallaye 17 a wasanni shida da suka buga na baya-bayan nan.

Masu sharhi akan wasannin kwallon kafa sun bayyana rashin katabus din da kungiyar ke fama da shi bai rasa nasaba da raunin da manyan ‘yan wasanta ke fama da shi da suka hada da gwarzon kwallon kafa na Duniya a kakar da ta wuce Rodri Hernandez, Jeremy Doku, Kobacic da sauransu.

Wanda dukkansu suna da rawar da za su taka a City idan aka yi la’akari da yadda dukkan wadannan ‘yan wasan suka taimaka wa City wajen lashe kofin gasar Firimiya a kakar wasannin da ta gabata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Manchester City
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jerin ‘Yan Wasa Uku Da Suka Zura Kwallaye 100 A Gasar Zakarun Turai

Next Post

Kano Ta Kaddamar Da Cibiyar Tafi-da-gidanka Ta Farko A Nijeriya Don Yi Wa Motoci Lasisi

Related

Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila
Wasanni

Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

10 hours ago
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu
Wasanni

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

2 days ago
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

2 days ago
Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
Wasanni

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

3 days ago
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
Wasanni

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

5 days ago
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Wasanni

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

6 days ago
Next Post
Kano Ta Kaddamar Da Cibiyar Tafi-da-gidanka Ta Farko A Nijeriya Don Yi Wa Motoci Lasisi

Kano Ta Kaddamar Da Cibiyar Tafi-da-gidanka Ta Farko A Nijeriya Don Yi Wa Motoci Lasisi

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.