• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Ta Gabatar Da bukukuwan Baje Kolin Al’adun Sin Na Musamman A “Palace of Nations” Da Kasar Masar

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Cmg
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Alhamis ne kafar CMG da ofishin MDD dake Geneva, da tawagar dindindin ta wakilan Sin dake Geneva, suka yi hadin gwiwar gabatar da bikin baje kolin al’adun Sin na musamman, a fadar kasashen duniya ta “palace of nations”. 

Shugaban CMG Shen Haixiong, da shugaban kwamitin raya al’adu na ofishin MDD dake Geneva Francesco Pisano, da kuma zaunannen wakilin Sin dake ofishin MDD dake Geneva da sauran kungiyoyin kasa da kasa dake Swizerland Chen Xu, sun halarci bikin tare da ba da jawabai.

  • Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana
  • Kamata Ya Yi Gwamnatin Amurka Ta Yi La’Akari Da Dalilan Karbuwar Gwamnan Jihar California A Kasar Sin

Wakiliyar musamman mai ba da shawara kan harkokin siyasa da huldar abokantaka, a ofishin babban jami’in MDD dake Geneva Lidiya Grigoreva, da dai sauran hukumomin kasa da kasa na MDD dake Geneva, da zaunannun wakilan kasashe fiye da 30 sun halarci bikin.

Cikin jawabin da ya gabatar, Shen Haixiong ya ce, al’adun Sin na bayyana mutuncin Sinawa, da kuma bayyana abubuwa mafi kyau a cikin al’adun bil Adama. Kaza lika kasar Sin na dukufa kan farfado da al’adun ta a sabon zamani. A matsayin kafa mafi girma dake watsa labarai a dukkanin fannoni na dandalolin daban-daban, Shen ya ce CMG na sauke nauyin dake wuyansa na shaida ci gaban al’adu, da ingiza mu’amalar al’adu, ban da wannan kuma, tana kokarin hada tunani da kimiyya da fasaha tare, ta yadda al’umommin kasa da kasa za su sada zumanta, da tutunbar juna, don zamanintar da al’ummar duniya cikin hadin kai.

Yayin bikin na musamman na wannan karo, mai taken “Mafarin al’adun Sin da ci gabansa”, an yi amfani da kimiyya da fasahar zamani, don jagorantar masu kallo, ta yadda za su fahimci al’adun Sin masu tsawon tarihin fiye da shekaru 5000, da ma yadda ake samun ci gaba bisa wannan tushe.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sannan a jiya Alhamis 26 ga wata ne, kafar CMG ta kuma gudanar da wani biki don kaddamar da nune-nunen “Journey Through Civilizations” wato hanyar fahimtar wayewar kai a cibiyar al’adun kasar Sin dake Alkahira, babban birnin kasar Masar. Mataimakin shugaban sashen fadakar da al’umma na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, wanda kuma shi ne shugaban CMG, Shen Haixiong ya yi jawabi ta kafar bidiyo.

A yayin jawabinsa, Shen Haixiong ya bayyana cewa, a cikin dogon tarihi, kyawawan wayewar kan kasar Sin da na tsohuwar kasar Masar sun ba da gudummawa sosai ga ci gaban wayewar kan dan Adam. Bisa ga kyakkyawan tsarin shawarar wayewar kai ta duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, jama’ar kasar Sin suna aiki tukuru don gina al’ummar kasar mai wayewar kai ta zamani, da sa kaimi ga neman sabon ci gaban wayewar kan dan Adam. Shen Haixiong ya kara da cewa, CMG zai tabbatar da aikin watsa labaru, da yin kirkire-kirkire, da yada wayewar kan kasar Sin, da karfafa mu’amalar al’adu tsakanin Sin da kasashen Larabawa, da sa kaimi ga yin shawarwari tsakanin al’ummomin Sin da kasashen Larabawa, da ba da hikimomi da karfi wajen bunkasa fahimtar juna da dankon zumunci tsakanin jama’ar Sin da kasashen Larabawa, da inganta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga Sin da kasashen Larabawa. (Masu Fassarawa: Amina Xu, Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CGTNCMGCRI Hausa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Wasan Kwaikwayon Na Zaben Kakakin Majalisar Wakilan Amurka Ta Kawo Karshe Ne? 

Next Post

Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

7 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

8 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

9 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

10 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

11 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

12 hours ago
Next Post
Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.