Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Crystal Palace ta samu babbar nasara a tarihinta bayan ta doke Manchester City da ci 1-0 a wasan ƙarshe na FA Cup da aka buga a filin Wembley da ke birnin Landan.
Wannan shi ne kofin farko da Crystal Palace ta taɓa lashe kofin tun bayan kafuwarta.
- Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
- Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
Eberechi Eze ne, ya zura ƙwallon da ta bai wa Palace nasara a minti na 16 da fara wasa.
Sabon ɗan wasan City, Omar Marmoush, ya samu dama mai kyau amma ya ɓarar da bugun fenariti a minti na 36.
Wannan kuma shi ne kofin ƙarshe da Manchester City ke fatan lashewa a wannan kakar.
Yanzu haka, ƙungiyar da Pep Guardiola ke jagoranta za ta kammala kakar ba tare da lashe kofi ba.
A wannan kakar kuwa, Liverpool ce ta lashe gasar Firimiya, yayin da Real Madrid ta fitar da Manchester City daga gasar Zakarun Turai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp