• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Anthrax: Yadda Masu Kiwon Dobbobi Suka Shiga Zullumi A Jos

by Sulaiman
2 years ago
Anthrax

Makiyaya a garin Jos da ke Jihar Filato, na ci gaba da nuna damuwarsu biyo bayan gano bullar cutar da ke harbin dabbobi (Anthrax) daga Jihar Neja.

“Akwai bukatar daukan matakan gaggawa yadda ya kamata domin dakile yaduwar cutar zuwa wannan gari namu na Jos.”
Haka zalika, Ma’aikatar aikin noma da raya karkara ta tarayya ce ta sanar da bullar wannan cuta da aka gano a Jihar ta Neja a makon da ya gabata, inda gano bullar cutar ya sanya makiyayan na garin Jos shiga matukar tashin hankali.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ja Hankulan Jama’a Kan Barkewar Cutar Anthrax A Ghana

Harwa yau, a ranar 14 ga watan Yulin 2023 ne Ofishin babban likitan dabbobi na kasa ya tabbatar da gano alamomin wannan cuta (Anthrax), a wata gona da ke Karamar Hukumar Suleja Jihar Nejan.

Wannan gona da ke garin Gajiri, daura da babban titin Abuja zuwa Kaduna a Karamar Hukumar Suleja, na dauke da rukunin dabbobi iri daban-daban da suka hada da Shanu, Akuyoyi da sauran makamantan su.
Biyo bayan bullar cutar a wannan gona ne, ya sanya wasu daga cikin makiyaya da sauran masu kiwo a garin na Jos shiga dimuwa da furgici tare da yin kiraye-kiraye don ganin an dakile ci gaba da yaduwarta.

“Ina da masaniya kwarai da gaske a kan wannan cuta, sannan ko shakka babu ina cikin matukar damuwa tun daga lokacin da na samu labarin tabbacin bullar ta a Jihar Neja,” a cewar wani makiyayi a Jos, Muhammad Rabi’u.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Muhammad ya ci gaba da cewa,“ ina kiwon shanu da tumaki, sannan a garken nasu nake kwana. Don haka, wajibi ne na kasance cikin firgici da damuwa.”
Daga nan ne, sai ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Filo da ta gaggauta daukar matakan da suka dace domin dakile yaduwar a fadin jihar baki-daya.

Shi ma wani makiyayin mai suna Babangida Musa ya bayyana nasa ra’ayin cewa, tun fil azal akwai wannan cutar, ba wai yanzu ba ne ta fara bayyana, sai dai kawai a kara tsaurara bincike tare da kokarin ganin an magance ta, ba ma a garin na Jos kadai ba, har ma fadin kasa baki-daya.

“Muna iya bakin kokarinmu na ganin wannan cuta ba ta ci gaba da yaduwa a wannan gari namu na Jos ba, sannan muna kuma yin kira ga Gwamnatin Jihar Filato, don sake ci gaba da dage damtse wajen daukar matan gaggawar day a kamata domin dakile yaduwar ta,” in ji Babangida.

Kazalika, wani makiyayin daga Jihar Neja mai suna Malam Muhammad ya karkare da cewa, “Bayan samun labarin bullar alamomin wannan cuta a Jihamu ta Neja, mun yi matukar kaduwar tare da shiga razani. Don haka, muke kira ga gwamnati da babbar murya don dakile ci gaba da yaduwar cutar a sauran gurare daban-daban.”

“Muna rokon Gwamnatin Jihar ta Filato da ta dakile yaduwar cutar zuwa cikin jihar, musamman ma cikin garin Jos da kewayensa. Muna kuma addu’ar kada cutar ta ci gaba da yaduwa sauran jihohin da ke a fadin wannan kasa,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
Noma Da Kiwo

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Noma Da Kiwo

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
Next Post
Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025
Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.