• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Anthrax: Yadda Masu Kiwon Dobbobi Suka Shiga Zullumi A Jos

by Sulaiman
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Cutar Anthrax: Yadda Masu Kiwon Dobbobi Suka Shiga Zullumi A Jos
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Makiyaya a garin Jos da ke Jihar Filato, na ci gaba da nuna damuwarsu biyo bayan gano bullar cutar da ke harbin dabbobi (Anthrax) daga Jihar Neja.

“Akwai bukatar daukan matakan gaggawa yadda ya kamata domin dakile yaduwar cutar zuwa wannan gari namu na Jos.”
Haka zalika, Ma’aikatar aikin noma da raya karkara ta tarayya ce ta sanar da bullar wannan cuta da aka gano a Jihar ta Neja a makon da ya gabata, inda gano bullar cutar ya sanya makiyayan na garin Jos shiga matukar tashin hankali.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ja Hankulan Jama’a Kan Barkewar Cutar Anthrax A Ghana

Harwa yau, a ranar 14 ga watan Yulin 2023 ne Ofishin babban likitan dabbobi na kasa ya tabbatar da gano alamomin wannan cuta (Anthrax), a wata gona da ke Karamar Hukumar Suleja Jihar Nejan.

Wannan gona da ke garin Gajiri, daura da babban titin Abuja zuwa Kaduna a Karamar Hukumar Suleja, na dauke da rukunin dabbobi iri daban-daban da suka hada da Shanu, Akuyoyi da sauran makamantan su.
Biyo bayan bullar cutar a wannan gona ne, ya sanya wasu daga cikin makiyaya da sauran masu kiwo a garin na Jos shiga dimuwa da furgici tare da yin kiraye-kiraye don ganin an dakile ci gaba da yaduwarta.

“Ina da masaniya kwarai da gaske a kan wannan cuta, sannan ko shakka babu ina cikin matukar damuwa tun daga lokacin da na samu labarin tabbacin bullar ta a Jihar Neja,” a cewar wani makiyayi a Jos, Muhammad Rabi’u.

Labarai Masu Nasaba

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

Muhammad ya ci gaba da cewa,“ ina kiwon shanu da tumaki, sannan a garken nasu nake kwana. Don haka, wajibi ne na kasance cikin firgici da damuwa.”
Daga nan ne, sai ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Filo da ta gaggauta daukar matakan da suka dace domin dakile yaduwar a fadin jihar baki-daya.

Shi ma wani makiyayin mai suna Babangida Musa ya bayyana nasa ra’ayin cewa, tun fil azal akwai wannan cutar, ba wai yanzu ba ne ta fara bayyana, sai dai kawai a kara tsaurara bincike tare da kokarin ganin an magance ta, ba ma a garin na Jos kadai ba, har ma fadin kasa baki-daya.

“Muna iya bakin kokarinmu na ganin wannan cuta ba ta ci gaba da yaduwa a wannan gari namu na Jos ba, sannan muna kuma yin kira ga Gwamnatin Jihar Filato, don sake ci gaba da dage damtse wajen daukar matan gaggawar day a kamata domin dakile yaduwar ta,” in ji Babangida.

Kazalika, wani makiyayin daga Jihar Neja mai suna Malam Muhammad ya karkare da cewa, “Bayan samun labarin bullar alamomin wannan cuta a Jihamu ta Neja, mun yi matukar kaduwar tare da shiga razani. Don haka, muke kira ga gwamnati da babbar murya don dakile ci gaba da yaduwar cutar a sauran gurare daban-daban.”

“Muna rokon Gwamnatin Jihar ta Filato da ta dakile yaduwar cutar zuwa cikin jihar, musamman ma cikin garin Jos da kewayensa. Muna kuma addu’ar kada cutar ta ci gaba da yaduwa sauran jihohin da ke a fadin wannan kasa,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hambararriyar Gwamnatin Bazoum Ta Nemi Faransa Ta Kwace Mulki Daga Sojojin Nijar

Next Post

Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

Related

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

2 days ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

3 days ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 week ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

2 weeks ago
Next Post
Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

Yadda Ake Sarrafa Rubutu Ta Word-Processing

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.