• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-Ɗumi: Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Nasarar Gwamna Inuwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamna inuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun ɗaukaka ƙara da ke zamanta a Abuja, a ranar Alhamis, ta tabbatar da nasarar da gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan jihar Gombe.

Kotun ta ce, kotun sauraron ƙararrakin zaɓe da ta tabbatar da sahihanci da ingancin zaɓen gwamnan Inuwa ta yi daidai domin shi ne halastaccen wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukaci Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • NNPP Ta Bukaci Majalisar Shari’a Ta Kasa Ta Binciki Hukuncin Da Aka Yanke Wa  Gwamna Yusuf

Kan hakan kotun ɗaukaka ƙarar ta kori ƙarar da jam’iyyar PDP da ɗan takararta Jibrin Barde suka shigar da ke ƙalubalantar hukuncin kotun sauraron ƙararrakin zaɓen na tabbatar da gwamna Inuwa na jam’iyyar APC.

Idan za a tuna dai hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta shelanta cewa Gwamna Muhammad Yahaya shi ne ya lashe zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris da ƙuri’u 342,821.

Yayin da ta ce Muhammad Jibrin Barde na PDP ya samu ƙuri’u 233,131 a zaɓen da aka fafata a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Amma Barde ya garza kotu domin ƙalubalantar nasarar Inuwa da iƙirarin cewa ba a bi dokar zabe ta 2022 ba wajen gudanar da zaɓen.

Sai dai kotun sauraron ƙararrakin zaɓen gwamnan jihar mai Alkalai uku a ƙarƙashin Justice S.B. Belgore, ta kori ƙarar da cewa bata da inganci.

Hakan ya sa ɗan takarar PDP ya sake garzayawa kotun ɗaukaka ƙara.

Kazalika, a ranar Alhamis ita ma kotun ɗaukaka ƙarar ta tabbatar da hukuncin kotun sauraron ƙararrakin zaɓen gwamnan jihar bisa cewa, korafin PDP bai da makama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna InuwaJihar GombeKotun Daukaka Kara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Nasarar Abdullahi Sule Bayan Kotun Sauraron Zabe Ta Tsigeshi

Next Post

Adamawa Za Ta Karbi Bakuncin Taron Gwamnonin Arewa Maso Gabas Na 9 A Gobe

Related

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

1 hour ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

2 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

3 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

8 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

19 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

21 hours ago
Next Post
Adamawa

Adamawa Za Ta Karbi Bakuncin Taron Gwamnonin Arewa Maso Gabas Na 9 A Gobe

LABARAI MASU NASABA

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.