ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da A Ce Ni Ba Dan Fim Ba Ne, Da Na Zama Malamin Addinin Musulunci -Baba Rabe

by Rabilu Sanusi Bena
8 months ago
Fim

Jarumin Kannywood Abubakar Waziri ko kuma Baba Rabe kamar yadda wasu ke kiranshi ya bayyana batutuwa da dama da su ka shafi jaruman fim, yadda suke gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum da kuma yadda mutane ke kallonsu, Baba Rabe a wata hira da ya yi da DW ya ce akwai bukatar malamai su shigo cikin harkar Kannywood ka’in da na’in domin yanzu wani lokaci ne da mutane sunfi mayar da hankalinsu wajen kallon fina-finai fiye da wa’azozin malaman musulunci.

Abubakar Waziri wanda ya ce shi haifaffen birnin Zaria ne a Jihar Kaduna, ya yi karatu a makarantu da dama har ma da Jami’ar Ahmadu Bello inda ya samu shaidar kammala karatun Diploma a bangaren Al’adun gargajiya, bayan harkar fim ni ma’aikacin gwamnati ne inda nike aiki da ‘Abuja Council For Art And Culture’, amma tunda farko na fara aiki a Jami’ar Ahmadu Bello a matsayin dan wasan kwaikwayo a sashen Al’adun Gargajiya na makarantar inji shi.

  • Nijeriya Za Ta Nuna Gyare-gyaren Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu A Taron Kasuwanci A Faransa
  • Taro Na Uku Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin Ya Yi Zama Na Biyu

Ya kara da cewar kafin shiga masana’antar Kannywood na yi tafiye tafiye da dama wajen wakiltar Nijeriya a kasashe daban-daban da su ka hada da Amurka, China, Afrika Ta Kudu, Korea Ta Arewa, Korea Ta Kudu da sauran kasashen waje duk dai a fannin raye raye da wasan kwaikwayo, kuma cikin ikon Allah yanzu kuma gani a masana’antar Kannywood a matsayin jarumi.

ADVERTISEMENT

Da yake amsa tambaya a kan yadda wasu ke daukar jaruman masana’antar Kannywood a matsayin wasu mutane masu girman kai, Abubakar Waziri ya ce ko kusa wannan magana ba gaskiya bace, misali mu jaruman fim da muka kasance abinda bature ke kira ‘public figure’, muma muna da abubuwan da muke son aiwatarwa a rayuwar yau da kullum, idan na fito daga gida idan ba na yi fuska na yi tafiya ta ba, mutane da dama kan zo wajena domin daukar hotuna ko kuma yi mani tambayoyi a kan wasu fina-finai da na yi.

Idan hakan ta faru wani lokacin mutum ba zai samu damar da zai aiwatar da abin da ya fito gida domin ya aiwatar ba, don haka kamata yayi mutane su fahimce mu a maimakon su koma gefe su na kiranmu da masu ji da kai, Waziri ya ci gaba da cewar wannan dalili ne ya sa mutane ke yi masu kudin goro a duk lokacin da wani daga cikinsu ya aikata abinda ba daidai ba a maimakon a dora ma wanda ya yi laifin shi kadai sai ace ai duka yan fim haka suke.

LABARAI MASU NASABA

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Daga karshe Abubakar Waziri Bado ya yi kira da a maimakon malamai su koma gefe su na zagi yan fim kamata ya yi ace su shigo cikin harkar a dama dasu, domin kuwa yanzu wani lokaci ne da ake ciki inda da dama mutane sun fi kallon fina-finai fiye da yadda su ke kallon karatuttukan malaman addini, saboda haka su shigo a hada karfi da karfe wajen kara tsaftace wannan masana’antar don kuwa ni ma kaina da ace ba jarumin fim bane ni , to da tabbas zan zama malamin addinin musulunci saboda ina matukar sha’awar ganin al’umma ta gyaru.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu
Nishadi

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala
Nishadi

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Nishadi

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Next Post
Yaushe Liverpool Za Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila?

Yaushe Liverpool Za Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila?

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.