• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Garba Shehu, kakakin tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya ce da Buhari ya sanya hannu kan dokar cire tallafin mai da yanzu shugaba Bola Ahmed Tinubu bai zama shugaban kasa ba.

Shehu, ya wallafa hakan ne a shafinsa na Twitter, inda ya bayyana dalilin da suka sanya Buhari bai sanya hannu kan dokar ba, da kuma yadda cire tallafin da Tinubu ya yi tun farkon hawansa mulki.

  • Amarya Da Kanwar Mijinta Sun Kubuta Daga Hannun Wadanda Suka Sace Su
  • Za Mu Kawar Da Matsalar Tsaro A Nijeriya -Nuhu Ribadu

Lamarin ya sanya wasu na tambayar me ya sa Buhari bai cire tallafin ba shekarun da ya kwashe a mulki.

Garba Shehu ya ce tabbas da APC ta fadi a zaben 2023 da Buhari ya cire tallafin man.

Ya ce, ya amince zai yi bayanin ne domin jama’a na tambaya kan cire tallafin da neman bayanin kan mene ne ya hana Buhari sanya hannun tare da muhawarar da suka biyo bayan sausa fasalin kudi.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ya ce kamata ya yi jam’iyya ta fito ta ba da amsa kan tambayoyin amma tilas dai ya sanya su fito su ce wani abu.

“Tabbas gwamnatin Tinubu da Shettima ta yi abun a yaba na cire tallafin mai. Mun yi imanin janye tallafin mai ba don shugaban kasa ne kawai ko don muradin kansa ba. Lamari ne da ya shafi al’ummar kasa.”

Ya ce batun janye tallafin mai da sauya takardun kudi lamari ne da suka janyo muhawara amma sai gwamnatin Buhari ta jingine batun janye tallafin mai zuwa lokacin da ya dace domin lamura su tafi daidai.

Ya kara da cewa lokacin da abubuwa suka yunkuro a lokacin zaben 2023 da gwamnatin Buhari ta dage kan cire tallafin mai da ‘yan kasa sun yi hannun riga da APC ta hanyar da za su kaurace wa zabar jam’iyyar.

“Amma sai muka yi la’akari da siyasarmu. Sai gwamnatin Buhari ta jingine batun cire tallafin mai domin jam’iyyar APC ta samunasara a zabe. Kuma hakan ya taimaka har aka samu nasara.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGarba ShehuTallafin Man FeturTinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sintiri, Sun Yi Wa Mata Fyade A Katsina

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

1 hour ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

2 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

2 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

3 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

6 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

6 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sintiri, Sun Yi Wa Mata Fyade A Katsina

'Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sintiri, Sun Yi Wa Mata Fyade A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.