• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: APC Ta Dage Ranar Fara Yakin Neman Zabenta

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Da Dumi-Dumi: APC Ta Dage Ranar Fara Yakin Neman Zabenta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, ya dage fara yakin neman zaben da aka shirya kaddamarwa a ranar Laraba.

Darakta-Janar na kwamitin yakin neman zaben Tinubu da Shettima, kuma gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

  • Masar Ta Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Na Gwaji A Makarantun Midil Na Kasar
  • An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

A cewarsa, an yi hakan ne domin daidaita jadawalin lokaci da jadawalin ayyuka ne domin ya yi daidai da harkokin duk masu hannu a cikin yakin neman zaben don samun nasararsa.

A cewarsa, nan ba da jimawa ba za a sanar da sabon lokacin da za a fara yakin neman zaben jam’iyyar.

Sanarwar ta ce; “Tun da farko mun shirya tattaki da addu’o’in zaman lafiya a ranar Laraba, 28 ga watan Satumba, 2022, don fara yakin neman zaben shugaban kasa na 2023 a hukumance. Mun kuma sanar da cewa mambobin kwamitin yakin neman zaben sun kai rahoto hedikwatar yakin neman zaben a ranar domin karbar wasikun nadi.

Labarai Masu Nasaba

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

“Duk da haka, saboda fadada jerin sunayen don samun karin masu ruwa da tsaki da bukatun cikin gida a APC, mun yanke shawarar daidaita jadawalin wadannan ayyuka domin tabbatar da cewa kowa yana cikin jirgin kafin a fara ayyukan a hukumance.

“Saboda haka, ayyukan da aka sanar a baya na ranar 28 ga Satumba ba za su ci gaba da kasancewa ba.

“A matsayinmu na jam’iyya mai mulki kuma mafi inganci a Nijeriya, mun fahimci sadaukarwa da fahimtar dimbin mambobinmu wadanda suka fi son sadaukar da kansu don wannan gagarumin aiki da ke gabanmu. Hakan kuma ya nuna irin tsananin soyayyar da ‘ya’yan jam’iyyar ke yi wa ’yan takararmu

“Za a sanar da sabon kwanan wata da jadawalin abubuwan da za su faru nan ba da jimawa ba”.

Idan ba a manta ba ranar 28 ga watan Satumba, 2022, ita ce ranar da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), ta ware ta ga jam’iyyu da ‘yan takara don fara yakin neman zabe a hukumance.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCINECShettimaSimon LalongTinubuYakin Neman ZabeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Kudin Shigar Kayayyakin Manhajar Masana’antun Sin A Watanni 7 Na Farkon Bana Ya Karu Da Kaso 8.7 Bisa Dari

Next Post

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

Related

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

44 minutes ago
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

2 hours ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

1 day ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

1 day ago
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

1 day ago
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
Manyan Labarai

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

1 day ago
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

May 31, 2025
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

May 31, 2025
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

May 31, 2025
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

May 31, 2025
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

May 31, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

May 31, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

May 31, 2025
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

May 31, 2025
Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.