• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Arteta

Kawo yanzu dai tuni wasu daga cikin tsofaffin ‘yan wasan kungiyar kwallon kafar ta Arsenal suka bayyana yadda kociyan kungiyar na yanzu, Mikel Arteta ya kawo gagarumin gyara a kungiyar musamman yadda take buga wasa a wannan lokacin.

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ita ce ta daya inda ta dauki hanyar lashe Premier League na bana karkashin Mikel Arteta, kofin da rabonta da shi tun kakar wasa ta 2003 zuwa 2004.

  • Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   
  • 2023: INEC Da ‘Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

Hakan yana nufin Arsenal ta sauya fasali tun daga salon buga wasa zuwa mai kayatarwa da fitar da kudi mai yawa wajen cefanen ‘yan wasa ba kamar yadda aka san kungiyar ba a baya.

A wannan kakar Arsenal tana jan ragamar Premier tana cikin wasannin European Cup da kuma FA Cup a kakar nan kuma wannan ci gaba da Arsenal ta samu ya samo asali daga daukar tsohon dan wasanta, wanda ta bai wa aikin horar da kungiyar ta kuma mara masa baya.

Arsenal ta dauki Mikel Arteta ranar 23 ga watan Disambar shekara ta 2019 daga Manchester City yana mataimakin mai koyar da Pep Guardiola, wanda shima dan asalin kasar Sipaniya ne.

LABARAI MASU NASABA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Arsenal ta kammala kakar wasan shekara ta 2018 zuwa 2019 a mataki na takwas, bayan da cutar Korona ta kai tsaiko a gasar da Liberpool ta lashe kofin sannan a kakar

Shekara ta 2020 zuwa 2021 ma Arsenal ta takwas ta kara yi, sakamakon kasa taka rawar gani, kuma wasan farko da Arteta ya fara jan ragama shi ne 1-1 da Bournemouth ranar 26 ga wasan Disambar 2019.

Amma tun daga nan Arteta ya lashe FA Cup a Arsenal da kai kungiyar Europa League, duk da cewar ya fuskanci kalubale a farkon aiki da wasu ke gannin ba zai iya ba a kakar wasan 2021 zuwa 2022.

A wannan kakar ne Arteta ya kare a mataki na biyar, bayan da a wasan karshe abokiyar hamayya Tottenham ta samu gurbin zuwa gasar cin kofin zakarun turai na Champions League.

To sai dai a bana Arsenal ta zama sabuwa, bayan da Arteta ya gama lakantar gasar Premier League ya kuma dora Arsenal kan turbar lashe kofin na bana duk da cewa wasu suna ganin kamar ba zai iya ba.

Arsenal mai kwantan wasa daya ta doke Manchester United ranar Lahadi a gasar Premier League da ci 3-2 – hakan ya sa kungiyar ta ci gaba da jan ragamar teburin gasar.

Dama Manchester United ce kadai ta ci Arsenal 3-1 a gasar Premier League a bana, sai kuma 0-0 da Newcastle United, wanda ba ta zura kwallo a raga ba a wasan haka kuma Arsenal ta tashi 1-1 a gasar Premier League a gidan Southampton.4

Rabon da Arsenal ta dauki Premier League tun kakar 2003 zuwa 2004 karkashin Arsene Wenger kuma cikin wasanni 19 da Arsenal ta buga a kakar nan ta ci 16 da canjaras biyu da rashin nasara daya, wadda take da maki 50.

Haka kuma kungiyar ta ci kwallo 45 aka zura mata 16 a raga, kenan tana da rarar 29 kawo yanzu kuma tun daga lokacin da Arteta ya karbi aikin kociyan Arsenal ya yi wasa 115 a Premier League da cin 65 da canjaras 18 da rashin nasara 32.

Haka kuma tsohon dan wasan na Arsenal ya ja ragamar kungiyar ta ci kwallo 193, sannan aka zura mata 124.

Ranar 9 ga watan Nuwamba Brighton ta fitar da Arsenal daga Carabao Cup da ci 3-1 a filin wasa na Emirates sannan ranar 27 ga watan nan Arsenal za ta fafata da Manchester City a FA Cup, wasan zai zama na hamayya kuma zakaran gwajin dafi ga kungiyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana
Wasanni

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars
Wasanni

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta
Labarai

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Next Post
Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.