• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu dai tuni wasu daga cikin tsofaffin ‘yan wasan kungiyar kwallon kafar ta Arsenal suka bayyana yadda kociyan kungiyar na yanzu, Mikel Arteta ya kawo gagarumin gyara a kungiyar musamman yadda take buga wasa a wannan lokacin.

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ita ce ta daya inda ta dauki hanyar lashe Premier League na bana karkashin Mikel Arteta, kofin da rabonta da shi tun kakar wasa ta 2003 zuwa 2004.

  • Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   
  • 2023: INEC Da ‘Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

Hakan yana nufin Arsenal ta sauya fasali tun daga salon buga wasa zuwa mai kayatarwa da fitar da kudi mai yawa wajen cefanen ‘yan wasa ba kamar yadda aka san kungiyar ba a baya.

A wannan kakar Arsenal tana jan ragamar Premier tana cikin wasannin European Cup da kuma FA Cup a kakar nan kuma wannan ci gaba da Arsenal ta samu ya samo asali daga daukar tsohon dan wasanta, wanda ta bai wa aikin horar da kungiyar ta kuma mara masa baya.

Arsenal ta dauki Mikel Arteta ranar 23 ga watan Disambar shekara ta 2019 daga Manchester City yana mataimakin mai koyar da Pep Guardiola, wanda shima dan asalin kasar Sipaniya ne.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

Arsenal ta kammala kakar wasan shekara ta 2018 zuwa 2019 a mataki na takwas, bayan da cutar Korona ta kai tsaiko a gasar da Liberpool ta lashe kofin sannan a kakar

Shekara ta 2020 zuwa 2021 ma Arsenal ta takwas ta kara yi, sakamakon kasa taka rawar gani, kuma wasan farko da Arteta ya fara jan ragama shi ne 1-1 da Bournemouth ranar 26 ga wasan Disambar 2019.

Amma tun daga nan Arteta ya lashe FA Cup a Arsenal da kai kungiyar Europa League, duk da cewar ya fuskanci kalubale a farkon aiki da wasu ke gannin ba zai iya ba a kakar wasan 2021 zuwa 2022.

A wannan kakar ne Arteta ya kare a mataki na biyar, bayan da a wasan karshe abokiyar hamayya Tottenham ta samu gurbin zuwa gasar cin kofin zakarun turai na Champions League.

To sai dai a bana Arsenal ta zama sabuwa, bayan da Arteta ya gama lakantar gasar Premier League ya kuma dora Arsenal kan turbar lashe kofin na bana duk da cewa wasu suna ganin kamar ba zai iya ba.

Arsenal mai kwantan wasa daya ta doke Manchester United ranar Lahadi a gasar Premier League da ci 3-2 – hakan ya sa kungiyar ta ci gaba da jan ragamar teburin gasar.

Dama Manchester United ce kadai ta ci Arsenal 3-1 a gasar Premier League a bana, sai kuma 0-0 da Newcastle United, wanda ba ta zura kwallo a raga ba a wasan haka kuma Arsenal ta tashi 1-1 a gasar Premier League a gidan Southampton.4

Rabon da Arsenal ta dauki Premier League tun kakar 2003 zuwa 2004 karkashin Arsene Wenger kuma cikin wasanni 19 da Arsenal ta buga a kakar nan ta ci 16 da canjaras biyu da rashin nasara daya, wadda take da maki 50.

Haka kuma kungiyar ta ci kwallo 45 aka zura mata 16 a raga, kenan tana da rarar 29 kawo yanzu kuma tun daga lokacin da Arteta ya karbi aikin kociyan Arsenal ya yi wasa 115 a Premier League da cin 65 da canjaras 18 da rashin nasara 32.

Haka kuma tsohon dan wasan na Arsenal ya ja ragamar kungiyar ta ci kwallo 193, sannan aka zura mata 124.

Ranar 9 ga watan Nuwamba Brighton ta fitar da Arsenal daga Carabao Cup da ci 3-1 a filin wasa na Emirates sannan ranar 27 ga watan nan Arsenal za ta fafata da Manchester City a FA Cup, wasan zai zama na hamayya kuma zakaran gwajin dafi ga kungiyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalArtetaGyaraKwallo
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

Next Post

Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Related

UEFA
Wasanni

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

24 hours ago
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila
Wasanni

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

1 day ago
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
Wasanni

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

3 days ago
De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
Wasanni

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

4 days ago
Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa
Wasanni

Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa

4 days ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

5 days ago
Next Post
Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

June 16, 2025
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

June 15, 2025
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

June 15, 2025
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

June 15, 2025
Dan Asalin Tudun Loess

Dan Asalin Tudun Loess

June 15, 2025
Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

June 15, 2025
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

June 15, 2025
Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.