• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?

byAbba Ibrahim Wada
3 years ago
Arteta

Kawo yanzu dai tuni wasu daga cikin tsofaffin ‘yan wasan kungiyar kwallon kafar ta Arsenal suka bayyana yadda kociyan kungiyar na yanzu, Mikel Arteta ya kawo gagarumin gyara a kungiyar musamman yadda take buga wasa a wannan lokacin.

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ita ce ta daya inda ta dauki hanyar lashe Premier League na bana karkashin Mikel Arteta, kofin da rabonta da shi tun kakar wasa ta 2003 zuwa 2004.

  • Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   
  • 2023: INEC Da ‘Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

Hakan yana nufin Arsenal ta sauya fasali tun daga salon buga wasa zuwa mai kayatarwa da fitar da kudi mai yawa wajen cefanen ‘yan wasa ba kamar yadda aka san kungiyar ba a baya.

A wannan kakar Arsenal tana jan ragamar Premier tana cikin wasannin European Cup da kuma FA Cup a kakar nan kuma wannan ci gaba da Arsenal ta samu ya samo asali daga daukar tsohon dan wasanta, wanda ta bai wa aikin horar da kungiyar ta kuma mara masa baya.

Arsenal ta dauki Mikel Arteta ranar 23 ga watan Disambar shekara ta 2019 daga Manchester City yana mataimakin mai koyar da Pep Guardiola, wanda shima dan asalin kasar Sipaniya ne.

LABARAI MASU NASABA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Arsenal ta kammala kakar wasan shekara ta 2018 zuwa 2019 a mataki na takwas, bayan da cutar Korona ta kai tsaiko a gasar da Liberpool ta lashe kofin sannan a kakar

Shekara ta 2020 zuwa 2021 ma Arsenal ta takwas ta kara yi, sakamakon kasa taka rawar gani, kuma wasan farko da Arteta ya fara jan ragama shi ne 1-1 da Bournemouth ranar 26 ga wasan Disambar 2019.

Amma tun daga nan Arteta ya lashe FA Cup a Arsenal da kai kungiyar Europa League, duk da cewar ya fuskanci kalubale a farkon aiki da wasu ke gannin ba zai iya ba a kakar wasan 2021 zuwa 2022.

A wannan kakar ne Arteta ya kare a mataki na biyar, bayan da a wasan karshe abokiyar hamayya Tottenham ta samu gurbin zuwa gasar cin kofin zakarun turai na Champions League.

To sai dai a bana Arsenal ta zama sabuwa, bayan da Arteta ya gama lakantar gasar Premier League ya kuma dora Arsenal kan turbar lashe kofin na bana duk da cewa wasu suna ganin kamar ba zai iya ba.

Arsenal mai kwantan wasa daya ta doke Manchester United ranar Lahadi a gasar Premier League da ci 3-2 – hakan ya sa kungiyar ta ci gaba da jan ragamar teburin gasar.

Dama Manchester United ce kadai ta ci Arsenal 3-1 a gasar Premier League a bana, sai kuma 0-0 da Newcastle United, wanda ba ta zura kwallo a raga ba a wasan haka kuma Arsenal ta tashi 1-1 a gasar Premier League a gidan Southampton.4

Rabon da Arsenal ta dauki Premier League tun kakar 2003 zuwa 2004 karkashin Arsene Wenger kuma cikin wasanni 19 da Arsenal ta buga a kakar nan ta ci 16 da canjaras biyu da rashin nasara daya, wadda take da maki 50.

Haka kuma kungiyar ta ci kwallo 45 aka zura mata 16 a raga, kenan tana da rarar 29 kawo yanzu kuma tun daga lokacin da Arteta ya karbi aikin kociyan Arsenal ya yi wasa 115 a Premier League da cin 65 da canjaras 18 da rashin nasara 32.

Haka kuma tsohon dan wasan na Arsenal ya ja ragamar kungiyar ta ci kwallo 193, sannan aka zura mata 124.

Ranar 9 ga watan Nuwamba Brighton ta fitar da Arsenal daga Carabao Cup da ci 3-1 a filin wasa na Emirates sannan ranar 27 ga watan nan Arsenal za ta fafata da Manchester City a FA Cup, wasan zai zama na hamayya kuma zakaran gwajin dafi ga kungiyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version