ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Arteta

Kawo yanzu dai tuni wasu daga cikin tsofaffin ‘yan wasan kungiyar kwallon kafar ta Arsenal suka bayyana yadda kociyan kungiyar na yanzu, Mikel Arteta ya kawo gagarumin gyara a kungiyar musamman yadda take buga wasa a wannan lokacin.

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ita ce ta daya inda ta dauki hanyar lashe Premier League na bana karkashin Mikel Arteta, kofin da rabonta da shi tun kakar wasa ta 2003 zuwa 2004.

  • Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   
  • 2023: INEC Da ‘Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

Hakan yana nufin Arsenal ta sauya fasali tun daga salon buga wasa zuwa mai kayatarwa da fitar da kudi mai yawa wajen cefanen ‘yan wasa ba kamar yadda aka san kungiyar ba a baya.

ADVERTISEMENT

A wannan kakar Arsenal tana jan ragamar Premier tana cikin wasannin European Cup da kuma FA Cup a kakar nan kuma wannan ci gaba da Arsenal ta samu ya samo asali daga daukar tsohon dan wasanta, wanda ta bai wa aikin horar da kungiyar ta kuma mara masa baya.

Arsenal ta dauki Mikel Arteta ranar 23 ga watan Disambar shekara ta 2019 daga Manchester City yana mataimakin mai koyar da Pep Guardiola, wanda shima dan asalin kasar Sipaniya ne.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Arsenal ta kammala kakar wasan shekara ta 2018 zuwa 2019 a mataki na takwas, bayan da cutar Korona ta kai tsaiko a gasar da Liberpool ta lashe kofin sannan a kakar

Shekara ta 2020 zuwa 2021 ma Arsenal ta takwas ta kara yi, sakamakon kasa taka rawar gani, kuma wasan farko da Arteta ya fara jan ragama shi ne 1-1 da Bournemouth ranar 26 ga wasan Disambar 2019.

Amma tun daga nan Arteta ya lashe FA Cup a Arsenal da kai kungiyar Europa League, duk da cewar ya fuskanci kalubale a farkon aiki da wasu ke gannin ba zai iya ba a kakar wasan 2021 zuwa 2022.

A wannan kakar ne Arteta ya kare a mataki na biyar, bayan da a wasan karshe abokiyar hamayya Tottenham ta samu gurbin zuwa gasar cin kofin zakarun turai na Champions League.

To sai dai a bana Arsenal ta zama sabuwa, bayan da Arteta ya gama lakantar gasar Premier League ya kuma dora Arsenal kan turbar lashe kofin na bana duk da cewa wasu suna ganin kamar ba zai iya ba.

Arsenal mai kwantan wasa daya ta doke Manchester United ranar Lahadi a gasar Premier League da ci 3-2 – hakan ya sa kungiyar ta ci gaba da jan ragamar teburin gasar.

Dama Manchester United ce kadai ta ci Arsenal 3-1 a gasar Premier League a bana, sai kuma 0-0 da Newcastle United, wanda ba ta zura kwallo a raga ba a wasan haka kuma Arsenal ta tashi 1-1 a gasar Premier League a gidan Southampton.4

Rabon da Arsenal ta dauki Premier League tun kakar 2003 zuwa 2004 karkashin Arsene Wenger kuma cikin wasanni 19 da Arsenal ta buga a kakar nan ta ci 16 da canjaras biyu da rashin nasara daya, wadda take da maki 50.

Haka kuma kungiyar ta ci kwallo 45 aka zura mata 16 a raga, kenan tana da rarar 29 kawo yanzu kuma tun daga lokacin da Arteta ya karbi aikin kociyan Arsenal ya yi wasa 115 a Premier League da cin 65 da canjaras 18 da rashin nasara 32.

Haka kuma tsohon dan wasan na Arsenal ya ja ragamar kungiyar ta ci kwallo 193, sannan aka zura mata 124.

Ranar 9 ga watan Nuwamba Brighton ta fitar da Arsenal daga Carabao Cup da ci 3-1 a filin wasa na Emirates sannan ranar 27 ga watan nan Arsenal za ta fafata da Manchester City a FA Cup, wasan zai zama na hamayya kuma zakaran gwajin dafi ga kungiyar.

Arteta
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.