ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Naja'atu

A halin da ake ciki kuma, Kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar APC ya mayar da martani kan bayanan Naja’atu kan watsi da dan takararsu na shugaban kasa Bola Tinubu, inda kwamitin ya ce Naja’atu Mohammed cikin banci ce a wurinsu wanda hakan ya sa suka kore ta.

Ya ce Naja’atu ta kasance tsohuwar daraktar hulda da kungiyoyin fararen hula a cikin kwamitin yakin neman zaben APC, amma saboda rashin kwarewa da fadace-fadace ne ya sa suka kore ta.

  • Kaso Mai Tsoka Na Ra’ayoyin Jama’a Ya Nuna Gamsuwa Da Nasarar Kasar Sin A Fannin Kandagarkin COVID-19
  • Karancin Man Fetur Da Sauya Kudade Shiri Ne Na Hana Zaben 2023 —Tinubu

A ranar 19 ga watan Janairun 2023, Naja’atu ta mika wasikar ajiye aiki ga shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Adamu, inda ta bayyana cewa ta ajiye mukaminta sakamakon matsalolin da Nijeriya ke fuskanta tana bukatar ci gaba da fafutukar samun ingantacciyar kasa.

ADVERTISEMENT

Amma a cikin wata sanarwa da mashawarci kan harkokin da suka shafi jama’a na yakin neman zaben APC, Mahmud Jega ya fitar, ya ce Naja’atu tana yaudarar ‘yan Nijeriya cewa ita da kanta ta ajiye aiki bayan kuma korar ta aka yi daga kwamitin yakin neman zaben na APC.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, Jega ya ce, “Tawagar yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu/Shettima ba ta samu takardar Naja’atu Mohammed na ajiye mukaminta a matsayin daraktar hulda da kungiyoyin fararen hula ba kafin a kore ta sakamakon rashin kwarewa da fadace-fadace, bayan ta yi watsi da gargadinmu na bai wa abokan adawa bayanan sirri.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

“Duk da ta kasance tana yaudarar ‘yan Nijeriya da cewa ita da kanta ta ajiye mukamin, wasikar korarta tana nan kan teburinta a ofishinta. Ta kasance cikon banci, tun lokacin da aka kore ta daga yakin neman zabe, take ta sambatu.

“Ta kasance ‘yar siyasa mara akida da take takama da kwarewa kuma ba ta da ita, kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na APC yana mamakin yadda Naja’atu wacce ta kasance ba likita ba amma take shakkun lafiyar Tinubu bayan likitoci sun tabbatar da cewa zai iya yin mulkin Nijeriya.

“Ko kungiyar likitoci za su kori magananta bisa zantar da hukuncin kan lafiya ba tare da yin gwaji ba.

“Duk da shi ne dan takarar shugaban kasa a 2023 da ya fi sauran ganin nasara a bayyana, amma Tinubu ya ziyarci mafi yawancin sassan kasar nan domin yin gaggamin yakin neman zabe da ganawa da kwararru da al’ummomi da kungiyoyin ‘yan kasuwa da kungiyoyin addinai,” in ji Jega.

Ya kara da cewa maganar da Naja’atu take yi cewa lokacin da ta tambayi Tinubu shirin da ya yi wa ‘yan arewa, sai ya ce bai da shi, wannan zance kawai ne.

“Tinubu yana da kyakkyawan tsari kan kasar nan, musamman matsalolin da suka shafi arewa. Lokacin da Tinubu ya halarci taron gamayyar kungiyoyin arewa a shekarar da ta gabata, ya bayyana musu irin abubuwan da ya tanada wa arewa.

“Muna kira ga magoya bayanmu a dukkan kasar nan su yi watsi da duk wata suka ga tafiyar Tinubu/Shettima ga ‘yan siyasa mara ka’ida.”

Naja'atu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki

July 3, 2026
Next Post
Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.