ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Naja'atu

A halin da ake ciki kuma, Kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar APC ya mayar da martani kan bayanan Naja’atu kan watsi da dan takararsu na shugaban kasa Bola Tinubu, inda kwamitin ya ce Naja’atu Mohammed cikin banci ce a wurinsu wanda hakan ya sa suka kore ta.

Ya ce Naja’atu ta kasance tsohuwar daraktar hulda da kungiyoyin fararen hula a cikin kwamitin yakin neman zaben APC, amma saboda rashin kwarewa da fadace-fadace ne ya sa suka kore ta.

  • Kaso Mai Tsoka Na Ra’ayoyin Jama’a Ya Nuna Gamsuwa Da Nasarar Kasar Sin A Fannin Kandagarkin COVID-19
  • Karancin Man Fetur Da Sauya Kudade Shiri Ne Na Hana Zaben 2023 —Tinubu

A ranar 19 ga watan Janairun 2023, Naja’atu ta mika wasikar ajiye aiki ga shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Adamu, inda ta bayyana cewa ta ajiye mukaminta sakamakon matsalolin da Nijeriya ke fuskanta tana bukatar ci gaba da fafutukar samun ingantacciyar kasa.

ADVERTISEMENT

Amma a cikin wata sanarwa da mashawarci kan harkokin da suka shafi jama’a na yakin neman zaben APC, Mahmud Jega ya fitar, ya ce Naja’atu tana yaudarar ‘yan Nijeriya cewa ita da kanta ta ajiye aiki bayan kuma korar ta aka yi daga kwamitin yakin neman zaben na APC.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, Jega ya ce, “Tawagar yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu/Shettima ba ta samu takardar Naja’atu Mohammed na ajiye mukaminta a matsayin daraktar hulda da kungiyoyin fararen hula ba kafin a kore ta sakamakon rashin kwarewa da fadace-fadace, bayan ta yi watsi da gargadinmu na bai wa abokan adawa bayanan sirri.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

“Duk da ta kasance tana yaudarar ‘yan Nijeriya da cewa ita da kanta ta ajiye mukamin, wasikar korarta tana nan kan teburinta a ofishinta. Ta kasance cikon banci, tun lokacin da aka kore ta daga yakin neman zabe, take ta sambatu.

“Ta kasance ‘yar siyasa mara akida da take takama da kwarewa kuma ba ta da ita, kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na APC yana mamakin yadda Naja’atu wacce ta kasance ba likita ba amma take shakkun lafiyar Tinubu bayan likitoci sun tabbatar da cewa zai iya yin mulkin Nijeriya.

“Ko kungiyar likitoci za su kori magananta bisa zantar da hukuncin kan lafiya ba tare da yin gwaji ba.

“Duk da shi ne dan takarar shugaban kasa a 2023 da ya fi sauran ganin nasara a bayyana, amma Tinubu ya ziyarci mafi yawancin sassan kasar nan domin yin gaggamin yakin neman zabe da ganawa da kwararru da al’ummomi da kungiyoyin ‘yan kasuwa da kungiyoyin addinai,” in ji Jega.

Ya kara da cewa maganar da Naja’atu take yi cewa lokacin da ta tambayi Tinubu shirin da ya yi wa ‘yan arewa, sai ya ce bai da shi, wannan zance kawai ne.

“Tinubu yana da kyakkyawan tsari kan kasar nan, musamman matsalolin da suka shafi arewa. Lokacin da Tinubu ya halarci taron gamayyar kungiyoyin arewa a shekarar da ta gabata, ya bayyana musu irin abubuwan da ya tanada wa arewa.

“Muna kira ga magoya bayanmu a dukkan kasar nan su yi watsi da duk wata suka ga tafiyar Tinubu/Shettima ga ‘yan siyasa mara ka’ida.”

Naja'atu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

June 12, 2026
Naja'atu
Manyan Labarai

June 12, 2026
Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya
Manyan Labarai

Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya

June 12, 2026
Next Post
Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.