ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Naja'atu

A halin da ake ciki kuma, Kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar APC ya mayar da martani kan bayanan Naja’atu kan watsi da dan takararsu na shugaban kasa Bola Tinubu, inda kwamitin ya ce Naja’atu Mohammed cikin banci ce a wurinsu wanda hakan ya sa suka kore ta.

Ya ce Naja’atu ta kasance tsohuwar daraktar hulda da kungiyoyin fararen hula a cikin kwamitin yakin neman zaben APC, amma saboda rashin kwarewa da fadace-fadace ne ya sa suka kore ta.

  • Kaso Mai Tsoka Na Ra’ayoyin Jama’a Ya Nuna Gamsuwa Da Nasarar Kasar Sin A Fannin Kandagarkin COVID-19
  • Karancin Man Fetur Da Sauya Kudade Shiri Ne Na Hana Zaben 2023 —Tinubu

A ranar 19 ga watan Janairun 2023, Naja’atu ta mika wasikar ajiye aiki ga shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Adamu, inda ta bayyana cewa ta ajiye mukaminta sakamakon matsalolin da Nijeriya ke fuskanta tana bukatar ci gaba da fafutukar samun ingantacciyar kasa.

ADVERTISEMENT

Amma a cikin wata sanarwa da mashawarci kan harkokin da suka shafi jama’a na yakin neman zaben APC, Mahmud Jega ya fitar, ya ce Naja’atu tana yaudarar ‘yan Nijeriya cewa ita da kanta ta ajiye aiki bayan kuma korar ta aka yi daga kwamitin yakin neman zaben na APC.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, Jega ya ce, “Tawagar yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu/Shettima ba ta samu takardar Naja’atu Mohammed na ajiye mukaminta a matsayin daraktar hulda da kungiyoyin fararen hula ba kafin a kore ta sakamakon rashin kwarewa da fadace-fadace, bayan ta yi watsi da gargadinmu na bai wa abokan adawa bayanan sirri.

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

“Duk da ta kasance tana yaudarar ‘yan Nijeriya da cewa ita da kanta ta ajiye mukamin, wasikar korarta tana nan kan teburinta a ofishinta. Ta kasance cikon banci, tun lokacin da aka kore ta daga yakin neman zabe, take ta sambatu.

“Ta kasance ‘yar siyasa mara akida da take takama da kwarewa kuma ba ta da ita, kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na APC yana mamakin yadda Naja’atu wacce ta kasance ba likita ba amma take shakkun lafiyar Tinubu bayan likitoci sun tabbatar da cewa zai iya yin mulkin Nijeriya.

“Ko kungiyar likitoci za su kori magananta bisa zantar da hukuncin kan lafiya ba tare da yin gwaji ba.

“Duk da shi ne dan takarar shugaban kasa a 2023 da ya fi sauran ganin nasara a bayyana, amma Tinubu ya ziyarci mafi yawancin sassan kasar nan domin yin gaggamin yakin neman zabe da ganawa da kwararru da al’ummomi da kungiyoyin ‘yan kasuwa da kungiyoyin addinai,” in ji Jega.

Ya kara da cewa maganar da Naja’atu take yi cewa lokacin da ta tambayi Tinubu shirin da ya yi wa ‘yan arewa, sai ya ce bai da shi, wannan zance kawai ne.

“Tinubu yana da kyakkyawan tsari kan kasar nan, musamman matsalolin da suka shafi arewa. Lokacin da Tinubu ya halarci taron gamayyar kungiyoyin arewa a shekarar da ta gabata, ya bayyana musu irin abubuwan da ya tanada wa arewa.

“Muna kira ga magoya bayanmu a dukkan kasar nan su yi watsi da duk wata suka ga tafiyar Tinubu/Shettima ga ‘yan siyasa mara ka’ida.”

Naja'atu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.