• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

by Sulaiman
4 hours ago
in Ra'ayi Riga
0
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sake haduwa da takwarorinsa na kasashen Kazakhstan da Kyrgyzstan da Tajikistan da Turkmenistan da kuma Uzbekistan a birnin Astana, inda suka halarci taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na biyu, don bude sabon babin hadin gwiwar kasashensu. 

Haduwarsu a wannan karo ta biyo bayan wacce suka yi a yayin taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na farko da aka gudanar a birnin Xi’an na kasar Sin shekaru biyu da suka wuce. A wannan karo kuma, kasashen sun fitar da sanarwar Astana game da taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na biyu, tare da rattaba hannu a kan yarjejeniyar kyakkyawar makwabtaka da abota da kuma hadin gwiwa na dindindin, baya ga shirye-shiryen hadin gwiwa har 110 da suka cimma.

  • IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 
  • Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Sai dai ma’anar taron ba ta tsaya ga wadannan nasarorin da aka cimma ba, abun da ya fi muhimmanci shi ne taron ya shaida inda za mu dosa musamman a yayin da duniyarmu ke fama da rashin tabbas da tashe-tashen hankula.

A yayin da shugaba Xi Jinping ke halartar taron, ya gabatar da jawabi, inda ya bayyana hadin gwiwar Sin da kasashen tsakiyar Asiya a matsayin “ruhin Sin da kasashen tsakiyar Asiya”, da ke “martaba juna da amincewa da juna da cin moriyar juna da kuma taimakon juna, da zamanantar da kowa ta tabbatar da ci gaba mai inganci.”

A bisa ruhin ne, Sin da kasashen nan biyar ke ta fadada hadin gwiwarsu, tare da karfafa hadin kansu don rungumar kyakkyawar makomarsu ta bai-daya. Idan mun duba, tun bayan taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na farko da aka gudanar a shekaru biyu da suka wuce, adadin cinikin da ke tsakanin Sin da kasashen nan biyar ya karu da kaso 35%, baya ga yadda suka inganta hadin gwiwarsu ta fannonin zuba jari da hakar ma’adinai ba tare da gurbata muhalli ba, da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha. Baya ga haka, a hukumance ne aka fara aikin gina layin dogon da ya ratsa kasashen Sin da Kyrgyzstan da Uzbekistan, kuma Sin da kasashen sun gina cibiyoyin al’adu a kasashen juna, kana Sin da Kazakhstan da kuma Uzbekistan sun cire wa al’ummomin juna bizar shiga kasashensu.

Labarai Masu Nasaba

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

A shekaru biyu da suka wuce, shugaban kasar Sin da takwarorinsa na kasashen nan biyar sun dasa wasu bishiyoyin ruman guda shida a birnin Xi’an, wadanda yanzu haka cike suke da furanni tare da alamanta hadin gwiwar kasashen mai cike da kyawawan nasarori, wadanda kuma suka shaida cewa, “hannu daya ba ya daukar jinka”, hada karfi da karfe ne zai kai ga inda aka dosa, kuma ba wanda ke iya cin nasara daga faduwar wasu, kuma za a iya tabbatar da nasara ga juna ne kurum idan aka zama tsintsiya madaurinki guda.

Yanzu haka, duniyarmu na fama da rikice-rikice da kariyar ciniki da ra’ayi na kashin kai da kuma siyasar nuna fin karfi. Amma bai kamata a mai da hannun agogon baya ba, kuma ba za a yarda da rarrabuwar kawuna a tsakanin al’ummomin duniya ba, kana ‘yan Adam bai kamata su koma irin rayuwar da masu karfi ke cin zalin masu karamin karfi kamar yadda aka yi a baya ba.

Daga birnin Xi’an zuwa Astana, Sin da kasashen tsakiyar Asiya sun samar da ruhin da ya amsa tambayar da zamaninmu ya aza mana, wato “me ya faru a duniyarmu, kuma me ya kamata mu yi”, wanda kuma ya karfafa mana niyyar kiyaye adalci da cin moriyar juna da samun nasara tare, don kiyaye zaman lafiyar duniya da tabbatar da ci gaban kasa da kasa baki daya. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Next Post

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

Related

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

1 day ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 days ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

5 days ago
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Ra'ayi Riga

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

1 week ago
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Ra'ayi Riga

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

1 week ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

2 weeks ago
Next Post
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba

An Kashe 'Yan Ta'adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu - Hedikwatar Tsaro 

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

June 19, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

June 19, 2025
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

June 19, 2025
Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

June 19, 2025
Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

June 19, 2025
Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

June 19, 2025
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

June 19, 2025
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.