Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Daliban Kwalejin Ilimi Ta Yobe 400 Sun Yi Rijista Da TRCN

by Tayo Adelaja
September 21, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela, Damaturu

Kimanin dalibai 400 ne wadanda suka kammala NCE a kwalejin ilimin jihar Yobe dake Gashuwa (Umar Suleiman College of Education, Gashu’a) suka sha rantsuwa da yin rijista da hukumar kwararrun malamai ta kasa ta Teachers’ Registration Council of Nigeria (TRCN), a karon farko da kwalejin ta gudanar da wannan shirin tun bayan kafuwar ta.

Farfesa Josiah Olusegun Ajiboye, shi ne shugaban hukumar TRCN wanda Daraktan kwararru da tsare-tsare a hukumar ya wakilta, Malam Adamu A. Bello a wajen bukin yiwa daliban rijista da rantsuwar kasancewar su halastattu malamai tare da mika musu takardar shaidar hukumar kwararrun malamai ta TRCN.

Mr Ajiboye ya yaba wa shugaban kwalejin, Malam Muhammad Gishiwa da cewar ya yi amfani da kwarewar sa wajen dawo da martabar makarantar, tare da bayyana shi da gwarzo wanda ya sadaukar da rayuwar sa wajen bunkasa ilimi. Sannan ya ce “kuma ta dalilin irin wannan jajircewa da salon shugabanci nagari ya jawo TRCN ta zo don yiwa kwararrun malamai kuma wadanda suka sami horo nagari rijista a karo na farko. Me yasa can baya bamu zo ba- muna rijistar kwararru ne kawai”. Ya bayyana.

“Dangane da wannan, TRCN ta kama turbar dawo da martabar sha’anin malanta bisa kan sahihiyar manufa domin ganin sashen ya amsa sunan sa na ingantaccen shirin samarda kwararru da kyakkyawan shugabanci mai ma’ana a kasar nan. Musamman yadda bangaren ya kasance babbar cibiyar dora kowacce al’umma bisa tsari mai kyau”. Malam Bello.

Shugaban hukumar ya kara da cewar, hukumar ta tsayu wajen bunkasa da kyautata ci gaban kwararrun malamai a farfajiyar cancanta, inda ya ce hakan zai baiwa malaman zarafin gano zurfin kwarewar sa tare da sanya shauki da karsashi a zukatan wadanda suka dauke su aikin koyarwa. Haka kuma ya gargadi sabbin malaman da cewa su kasance jekadu kuma malamai nagari su guji bin son zuciya da zai shafawa malanta bakin fenti da karya dokokin dake shimfide a dokar TRCN (Act Cap T3 of 2004), ya ce bi ta kan dokar na iya jawo kora da dauri ga mai laifin.

Da yake tofa nashi albarkacin baki, shugaban kwalejin Malam Muhammad Gishiwa ya yaba da namijin kokarin hukumar TRCN da” na yi imanin cewar ta dalilin rashin ingantaccen tsarin sanin ina aka dosa a tsarin malanta ya haifar da tunanin kirkiro wannan cibiya, domin dawo da martabar fannin, kuma bisa ga dukkan alamu tafiya ta mike wajen kaiwa ga kwalliya ta biya kudin sabulu”. Inji Malam Gishiwa.

“Cibiyoyin horas da malamai kamar irin tamu, suna aiki tukuru tare da ganin sun ba maras da kunya dangane da aiwatar da manufofin gwamnati a kan ilimi a karkashin hukumar kula da kwalejiji ta kasa(NCCE ), wajen samar da nagartattu kuma kwararrun malamai domin bayar da kulawa ta musamman a kananan makarantun mu”.

Malam Muhammad Gishiwa ya sake nanata cewar ”ko shakka babu, muddin wadannan kwararru kuma horarrun malamai zasu iya taka kowacce marhala a karkashin kulawar TRCN, kuma bisa hakikanin gaskiya, za a samu ci gaba mai ma’ana nan gaba a sha’anin malamanta a Nijeriya”. Ya nanata.

SendShareTweetShare
Previous Post

Al-Makura Ya Gargadi ’Yan Nijeriya Da Su Guji Furta Kalaman Kiyayya

Next Post

Nasarawa Ta Yi Sabon Kwamishinan ’Yan Sanda

RelatedPosts

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

by Muhammad
2 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnatin Jihar Gombe ta sanar dokar...

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

by Daurawa Daurawa
4 hours ago
0

Daga Rabi'u Ali Indabawa, Abuja Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya,...

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

by Muhammad
8 hours ago
0

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi kira...

Next Post

Nasarawa Ta Yi Sabon Kwamishinan ’Yan Sanda

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version