• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
Abinci

Masana da masu ruwa da tsaki a lamuran da suka shafi noma sun bayyana muhimman dalilin da suka sabbaba Nijeriya ke tsintar kanta cikin matsalolin karancin abinci.

 

Masanan sun ce a baya dai, bangaren noma shi ke jan ragamar tattalin arzikin Nijeriya, yayin da manoma a jihohi da shiyyoyi suka maida hankali ka-in-da-na-in wajen noma kayan abinci a yankunansu da hakan ya bayar da damar wadata garuruwansu da kayan abinci har ma su fitar zuwa waje.

  • Nazari Kan Samun Kudin Shiga Ta Hanyar Kiwon Kajin Gida
  • Masana Sun Nuna Damuwarsu Kan Yadda Ake Takura Wa Masu Zuba Jari Da Ka’idoji

Sun kuma yi la’akari da yadda manoman arewa suka fi kwarewa wajen noma shinkafa, masara, gyada kuma wadannan abincin ana samar da su sosai, wadanda su ne ma aka fi amfani da su, yayin da a kudu maso yamma kuma suka gwanance wajen noman koko da rogo, inda yankin kudu maso gabas suka rungumi samar da manja.

 

LABARAI MASU NASABA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

A cewar masanan, kasar ta samu kanta cikin cin gajiyar wadannan abubuwan da ake noma, amma yanzu lamarin na neman zama babbar matsala, inda ake samun karancin abinci, yayin da manoma da dama suka daina noma, kamfanoni su na fuskantar karancin samun kayayyakin amfani, sannan ita kuma gwamnati ta dukufa wajen yaki da matsalar tsaro da rigingimun siyasa.

 

Shugaban kungiyar manoma ta COMAFAS, Dakta Austine Maduka, ya ce, samun danyen mai da ake yi a Nijeriya ya sanya kasar ta sakankance da lamarin samar da kayan noma, inda ya ce, hakan kuma ya janyo matasa da dama sun bar garuruwansu da ke kauyuka domin zuwa birane neman aiki a bangaren mai da iskar gas, yayin da suka bar harkokin noma kuma.

 

Ya kuma nuna cewa rashin nagartattun tsare-tsaren gwamnati kan noma sun kara shafan lamarin samar da kayan abinci. Ya nuna takaicinsa, kan yadda shugabannin da aka yi a Nijeriya ba su iya ci gaba da tafiyar da tsare-tsaren shugabannin da suka karbi mulki a hannunsu, inda ya nuna cewa kowani shugaba ya zo sai ya ce zai yi nasa tsarin daban, yayin da hakan ke maida hannun agogo baya.

 

Ya kuma nuna cewa wasu shugabannin sun fi maida hankali kan nau’ikan kayan abinci da ake cirewa a arewa, yayin da wasu tsare-tsaren gwamnatocin baya kuma suka fi daukan hankali a irin kayan abincin da ake nomawa a kudanci.

 

Kazalika, ya nemi gwamnatin tarayya ta hannun ma’aikatar ruwa da ta bude wasu karin dam-dam da manoma za suke samun ruwa a kowace shekara yadda suke bukata. Ya ce, kacokam an dogara ne kawai da noma in an samu damina, yayin da noman rani kuma ba su da yawa.

 

Ya ce, ya kamata gwamnati ta tanada ruwan da ke malala a kasa, musamman wanda yake zama ambaliya ta yadda manoma za su samu na amfani da shi bayan damina, sannan ta kara samar da filayen noma a jihohi da kananan hukumomi.

 

Sai ya nuna cewa wasu gwamnonin su na kokari sosai wajen taimaka wa harkokin manoma da dukkanin abubuwan da ake bukatu a bangaren noma, ya buga misali da Jihar Jigawa, ya ce kokarin da gwamnatin Jigawa ke yi a bangaren noma za a ga alfanunsa nan gaba.

 

Ya ce, gwamnatin Inugu da Anambra su ma a kwanan nan sun rabar wa manoma da iri da kayan noma. Ya ce, akwai bukatar gwamnatoci su sanya a ransu wajen maida hankali kan yadda za a yi noma da yadda za a girbe amfanin noma.

 

A nasa bangaren, kwararre kan noman rogo daga Jihar Ogun, Kunle Abdul ya soki gwamnatin jihar da rashin kyawawan tsare-tsaren da za su ciyar da harkokin noma gaba, inda ta kasa koyi da yunkurin gwamnatin tarayya na inganta harkokin noma.

 

Shi kuwa, kwararre kan abinci da wadatar abinci, Hammed Jimoh ya ce, manyan matsalolin da Nijeriya ke fuskanta a bangaren samar da abinci sun hada har da matsalar rashin tsaro da ya janyo salwantuwar manoma da dama a kasar nan, musamman a jihohin Borno, Benuwai, Zamfara, Kaduna da sauran jihohi, lamarin da ke kara sanyawa wasu manoma kaurace wa gonakai domin tsira da rayukansu.

 

“Idan kuka nazarci yankunan da matsalolin tsaro suka fi kamari a halin yanzu a Nijeriya, za a fahimci jihohin nan su ne masu samar da abinci mafi yawa a baya, kamar jihohin Borno, Katsina, Kaduna da Benuwai.”

 

Jimoh ya kuma ce sauyin yanayi shi ma na barazana ga wadatar samar da abinci a Nijeriya, “An fi dogara da ruwan damina wajen noma a Nijeriya, sauyin yanayi na canzawa. An gaya min cewa kudu maso yamma kusan sama da watanni biyu ba su samu ruwan sama ba, don haka yanayin na canzawa.

 

“Muddin in za mu dogara kacokam kan sai mun samu ruwan sama mu yi noma, gaskiya za mu yi ta samun matsala, saboda ba za mu dunga samun abun da muke so ba, yana da kyau a nemo wasu hanyoyin na daban.”

 

Wani manomi a Jihar Kogi, Sunday Audu ya zargi gwamnatin da kin taimaka wa manoma balle manoma su samu kyautata nomansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya
Labarai

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Nijeriya
Labarai

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Next Post
A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

LABARAI MASU NASABA

peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.