• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
Dalilan Da Suka Sabbaba Karancin Abinci A Nijeriya — Masana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana da masu ruwa da tsaki a lamuran da suka shafi noma sun bayyana muhimman dalilin da suka sabbaba Nijeriya ke tsintar kanta cikin matsalolin karancin abinci.

 

Masanan sun ce a baya dai, bangaren noma shi ke jan ragamar tattalin arzikin Nijeriya, yayin da manoma a jihohi da shiyyoyi suka maida hankali ka-in-da-na-in wajen noma kayan abinci a yankunansu da hakan ya bayar da damar wadata garuruwansu da kayan abinci har ma su fitar zuwa waje.

  • Nazari Kan Samun Kudin Shiga Ta Hanyar Kiwon Kajin Gida
  • Masana Sun Nuna Damuwarsu Kan Yadda Ake Takura Wa Masu Zuba Jari Da Ka’idoji

Sun kuma yi la’akari da yadda manoman arewa suka fi kwarewa wajen noma shinkafa, masara, gyada kuma wadannan abincin ana samar da su sosai, wadanda su ne ma aka fi amfani da su, yayin da a kudu maso yamma kuma suka gwanance wajen noman koko da rogo, inda yankin kudu maso gabas suka rungumi samar da manja.

 

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

A cewar masanan, kasar ta samu kanta cikin cin gajiyar wadannan abubuwan da ake noma, amma yanzu lamarin na neman zama babbar matsala, inda ake samun karancin abinci, yayin da manoma da dama suka daina noma, kamfanoni su na fuskantar karancin samun kayayyakin amfani, sannan ita kuma gwamnati ta dukufa wajen yaki da matsalar tsaro da rigingimun siyasa.

 

Shugaban kungiyar manoma ta COMAFAS, Dakta Austine Maduka, ya ce, samun danyen mai da ake yi a Nijeriya ya sanya kasar ta sakankance da lamarin samar da kayan noma, inda ya ce, hakan kuma ya janyo matasa da dama sun bar garuruwansu da ke kauyuka domin zuwa birane neman aiki a bangaren mai da iskar gas, yayin da suka bar harkokin noma kuma.

 

Ya kuma nuna cewa rashin nagartattun tsare-tsaren gwamnati kan noma sun kara shafan lamarin samar da kayan abinci. Ya nuna takaicinsa, kan yadda shugabannin da aka yi a Nijeriya ba su iya ci gaba da tafiyar da tsare-tsaren shugabannin da suka karbi mulki a hannunsu, inda ya nuna cewa kowani shugaba ya zo sai ya ce zai yi nasa tsarin daban, yayin da hakan ke maida hannun agogo baya.

 

Ya kuma nuna cewa wasu shugabannin sun fi maida hankali kan nau’ikan kayan abinci da ake cirewa a arewa, yayin da wasu tsare-tsaren gwamnatocin baya kuma suka fi daukan hankali a irin kayan abincin da ake nomawa a kudanci.

 

Kazalika, ya nemi gwamnatin tarayya ta hannun ma’aikatar ruwa da ta bude wasu karin dam-dam da manoma za suke samun ruwa a kowace shekara yadda suke bukata. Ya ce, kacokam an dogara ne kawai da noma in an samu damina, yayin da noman rani kuma ba su da yawa.

 

Ya ce, ya kamata gwamnati ta tanada ruwan da ke malala a kasa, musamman wanda yake zama ambaliya ta yadda manoma za su samu na amfani da shi bayan damina, sannan ta kara samar da filayen noma a jihohi da kananan hukumomi.

 

Sai ya nuna cewa wasu gwamnonin su na kokari sosai wajen taimaka wa harkokin manoma da dukkanin abubuwan da ake bukatu a bangaren noma, ya buga misali da Jihar Jigawa, ya ce kokarin da gwamnatin Jigawa ke yi a bangaren noma za a ga alfanunsa nan gaba.

 

Ya ce, gwamnatin Inugu da Anambra su ma a kwanan nan sun rabar wa manoma da iri da kayan noma. Ya ce, akwai bukatar gwamnatoci su sanya a ransu wajen maida hankali kan yadda za a yi noma da yadda za a girbe amfanin noma.

 

A nasa bangaren, kwararre kan noman rogo daga Jihar Ogun, Kunle Abdul ya soki gwamnatin jihar da rashin kyawawan tsare-tsaren da za su ciyar da harkokin noma gaba, inda ta kasa koyi da yunkurin gwamnatin tarayya na inganta harkokin noma.

 

Shi kuwa, kwararre kan abinci da wadatar abinci, Hammed Jimoh ya ce, manyan matsalolin da Nijeriya ke fuskanta a bangaren samar da abinci sun hada har da matsalar rashin tsaro da ya janyo salwantuwar manoma da dama a kasar nan, musamman a jihohin Borno, Benuwai, Zamfara, Kaduna da sauran jihohi, lamarin da ke kara sanyawa wasu manoma kaurace wa gonakai domin tsira da rayukansu.

 

“Idan kuka nazarci yankunan da matsalolin tsaro suka fi kamari a halin yanzu a Nijeriya, za a fahimci jihohin nan su ne masu samar da abinci mafi yawa a baya, kamar jihohin Borno, Katsina, Kaduna da Benuwai.”

 

Jimoh ya kuma ce sauyin yanayi shi ma na barazana ga wadatar samar da abinci a Nijeriya, “An fi dogara da ruwan damina wajen noma a Nijeriya, sauyin yanayi na canzawa. An gaya min cewa kudu maso yamma kusan sama da watanni biyu ba su samu ruwan sama ba, don haka yanayin na canzawa.

 

“Muddin in za mu dogara kacokam kan sai mun samu ruwan sama mu yi noma, gaskiya za mu yi ta samun matsala, saboda ba za mu dunga samun abun da muke so ba, yana da kyau a nemo wasu hanyoyin na daban.”

 

Wani manomi a Jihar Kogi, Sunday Audu ya zargi gwamnatin da kin taimaka wa manoma balle manoma su samu kyautata nomansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 5 Da Karbar Wadanda Suka Yi Saranda 44 A Borno

Next Post

A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

8 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

9 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

10 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

13 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

15 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

16 hours ago
Next Post
A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.