• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suke Sa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Ci Gaba Da Tafka Asara A Halin Yanzu

by Abubakar Abba
5 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Dalilan Da Suke Sa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Ci Gaba Da Tafka Asara A Halin Yanzu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin halin da ake ciki yanzu, akasarin masu kiwon Kajin gidan gona, na ci gaba da fuskantar kalubalen da ya hada da rage yawan samun masu sayen Kwai.

Kazalika, suna fuskantar kalubalen dakatar da wasu shirye-shiryen gwamnati, kamar na bai wa daliban makarantar firamare Kwai da sauran shirye-shiryen da gwamnatin ta kirkiro, wadanda suka shafi bangaren bayar da Kwan.

  • Bai Wa Shanu Guba: Sojoji Sun Shiga Tsakani Domin Dakile Yunkurin Ramuwar Gayya A Filato
  • Ina Dalilin Da Ya Sa Cinikin Shige Da Fice Na Kasar Sin Ke Samun Bunkasuwa Mai Dorewa Ba Tare Da Tangarda Ba?

Kusan za a iya cewa, wadannan matsaloli da masu kiwon Kajin gidan gona ke fuskanta, na kara ta’azzara ne sakamakon ba su kayan ayyukan da za su iya adana Kwan har zuwa wani dogon lokaci, musamman duba da yanayin zafin da ake fuskanta a fadin wannan kasa, ya kara tabarbara al’amuran kiwon baki-daya.

Wadannan matsaloli, sun jawo wa masu kiwon Kajin na gidan gona, sayar da Kwansu cikin farashi mai rahusa, musamman don guje wa tabka asara.

Ya danganta da yadda girman Kwan yake, misali, a babban birnin tarayyar Abuja, a kananan shaguna yanzu, ana sayar da duk kiret daya daga tsakanin Naira 5,000 zuwa Naira 6,500.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Bugu da kari, saboda karancin masu sayen Kwan, musamman sakamakon matsin tattalin arziki da ake fama da shi, ana kara samun masu sayen Kwan don amfani da shi, wanda hakan ya sanya ake ci gaba da samun Kwan da ba a sayar ba.

Misali, a makwanni biyu da suka gabata a garin Jos, an samu matukar raguwar farashin Kwan, inda ake sayar da shi kasa da Naira 3,900 zuwa Naira 4,000.

Sai dai, a wannan makon an dan samu karin farashin, wanda ya kai daga Naira 4,200 zuwa 4,300.

Daya daga cikin irin wadannan masu kiwon Kajin na gidan gona, Muhammad Bello Ibrahim, ya bayyana bacin ransa kan yadda wannan matsala ke ci gaba da faruwa.

“Masu sana’ar kiwon Kajin a yanzu haka, suna ci gaba da fuskantar kalubalen rashin samun masu sayen Kwan,” in ji Bello.

Ya ci gaba da cewa, a baya; a karkashin shirye-shiryen ciyarwa na gwamnati, ana karfafa wa wasu jihohin sayen Kwan da ake bai wa ‘yan makarantar firamere, domin amfanin marasa lafiya da aka kwantar a asibiti da kuma amfanin wadanda ake tsare da su a gidan gyaran hali, amma kusan yanzu, shirye-shiryen sun tsaya cak.

Bisa wani bincike da aka gudanar a garin na Jos, duk da raguwar da aka samu na farashin Kwan, ana ci gaba da fuskatar karancin masu saye, wanda kuma hakan ya sa ake samun kwantan Kwan.

Hakan na kuma faruwa ne a yayin da ake ci gaba da fuskantar tsananin zafi, a jihohin kasar ciki har da garin na Jos.

Wata mai kiwon Kajin gidan gona a Jihar Filato, Nanji Gambo-Oke, ta sanar da cewa, kiwon Kajin a jihar, na fuskanta babban kalubale.

A cewar tata, kashi 80 cikin dari na Kwan da ake kyankyashewa a jihar, makwabtan jihar ne ke zuwa saye, ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

Ta kara da cewa, a bangaren gwamnatin jihar kuma tana nuna halin ko in kula dangane da kwantan Kwan da masu kiwon a jihar ke ci gaba da samu.

“Babu wani dauki da masu kiwon Kajin gidan gonar a jihar ke samu daga bangaren gwamnatin jihar, wanda hakan ke ci gaba da jefa su cikin halin tsaka mai wuya”, in ji Nanji.

Sai dai, Shugabar Kungiyar Masu Kiwon Kajin Gidan Gonar, reshen jihar Madam Shinkur Angela Jima, ta sanar da cewa, gwamnatin jihar na nuna goyon baya ga fannin.

Ta kara da cewa, a yanzu haka, gwamnatin na kokarin samar da tsare-tsaren da za ta tallafa wa masu kiwon a jihar.

Bugu da kari, a Jihar Neja ma, masu kiwon Kajin na ci gaba da fuskantar kalubalen rashin samun masu sayen Kwan da kuma rashin samun kayan aiki na zamani, wanda hakan ke jawo lalacewar Kwan nasu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AsaraKajiKiwo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ainihin Jarin Wajen Da Sin Ta Yi Amfani Da Shi Ya Karu Da Kaso 13.2% A Maris Na Bana

Next Post

Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

4 hours ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

3 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

3 weeks ago
Next Post
Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin

Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.